Wike Ya Shiga Matsala Yayin da Ake Zarge Shi Da Aikata Wani Mummunan Laifi

Wike Ya Shiga Matsala Yayin da Ake Zarge Shi Da Aikata Wani Mummunan Laifi

  • Rigingimun da suka dabaibaye Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, sun ƙara ɗaukar zafi
  • Ana zargin tsohon gwamnan na jihar Rivers cewa ya kitsa kisan wani babban jami'in ƴan sanda
  • An kuma tuhumi Wike da wawushe dala miliyan 300 na sake gina yankin Ogoni a jihar Rivers

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Rivers - Boma Goodhead, ƴar majalisar wakilai daga jihar Rivers, ta yi iƙirarin cewa Nyesom Wike ne ke da alhakin kitsa kisan Bako Angbashim, DPO na ƙaramar hukumar Ahoada ta Gabas a jihar.

A wani faifan bidiyo da ya yaɗu a shafukan sada zumunta, Goodhead mai wakiltar mazabar Asari-Toru a jihar ta zargi tsohon gwamnan na jihar Rivers da hannu a mutuwar Angbashim.

Kara karanta wannan

Wata Sabuwa: Ana zargin Shugaba Tinubu da rura wutar rikici a jihar PDP, bayani sun fito

An zargi Wike da kisan DPO a Rivers
Yar majalisa ta zargi Wike da wawushe $300m Hoto: Nyesom Ezenwo Wike
Asali: Facebook

Ƴar jam’iyyar PDP mai shekaru 53, ta yi kira ga hukumomin tsaro da su binciki Wike tare da tuhumarsa kan lamarin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A ranar Juma’a, 8 ga watan Satumba, DPO ɗin ya rasa ransa a wata arangama da wasu ƴan ƙungiyar asiri.

Rundunar ƴan sandan jihar ta kama wasu mutane da suke ganin suna da alhakin kisan, amma Goodhead ta yi iƙirarin cewa Wike ya ɗauki nauyin lamarin.

Ana zargin Wike da wawure dala miliyan 300

Goodhead, ƴar majalisar tarayya kuma ƴar uwar tsohon shugaban tsagerun Neja Delta, Asari Dokubo, ta zargi Wike da yin rashin nasara a rumfar zaɓensa a zaɓen shugaban ƙasa.

Bugu da ƙari, ta yi zargin cewa Wike ya wawure dala miliyan 300 da aka ware domin al'ummar Ogoni, inda ta bayyana ministan na Abuja a matsayin "wanda ya saba da ƙarya kuma mayaudari."

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP ya maida zazzafan martani yayin da ake shirin tsige shi daga kan mulki

A cewarta, Wike ya yi alfahari da cewa yana da iko da ɓangaren shari’a da fadar shugaban ƙasa.

Fubara Ya Umarci Kwamishinoni Su Yi Murabus

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya umarci dukkan kwamishinonin da ministan Abuja, Nyesom Wike, ya naɗa su miƙa takardun murabus.

Wannan umarnin na zuwa ne daidai lokacin da rikicinsa da magabacin na sa ya ƙara ɗaukar zafi a jihar ta Rivers.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng