Innalillahi: Babban Limamin Masallacin Tede Kuma Shugaban Majalisar Malamai Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Innalillahi: Babban Limamin Masallacin Tede Kuma Shugaban Majalisar Malamai Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

  • An shiga jimami yayin da wani babban limami a garin Tede da ke karamar hukumar Atisbo na jihar Oyo ya rasu
  • Marigayin mai suna Alhaji Ahmad Tijani Adedigba kafin rasuwarshi shi ne babban limamin Tede
  • Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya nuna alhininsa kan wannan babbar rashi inda ya yi addu’ar Allah ya masa rahama

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Oyo – Babban limamin Tede da ke a cikin jihar Oyo, Alhaji Ahmad Tijani Adedigba ya riga mu gidan gaskiya.

Kafin rasuwar marigayin, shi ne shugaban kungiyar limamai da malamai da ke Oke Ogun.

Babban limamin masallacin Tede ya riga mu gidan gaskiya
Marigayin ya rasu bayan fama da jinya a jihar Oyo. Hoto: @Oyoaffairs.
Asali: Facebook

Martanin Gwamna Makinde kan rasuwar

Yayin da ya ke tura sakon jaje, Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya bayyana rasuwar marigayin a matsayin babban rashi.

Kara karanta wannan

An kawo wata dabarar tsige Gwamnan PDP, Magoya bayan Minista ba su hakura ba

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Makinde ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi 10 ga watan Disamba, cewar Independent News.

Gwamnan ya ce tabbas al’ummar Musulmi sun yi babban rashi da rasuwar malamin da ya ba da gudunmawa ga addini.

Sanarwar ta ce:

“Cikin jimami na samu labarin rasuwar Alhaji Ahmad Tijani, shugaban gamayyar limamai da kuma malamai a Tede da ke karamar hukumar Atisbo a jihar.
“Marigayin mutum ne mai son zaman lafiya wanda ya ba da gudunmawa wurin jagorantar limamai da malamai da inganta addini a Oke Ogun.
“Yayin da mu ke mika lamarin mu ga Allah, mu na addu’ar ubangiji ya ba shi aljannar Firdausi da sauran wadanda su ka mutu.”

Dan tsohon Alaafin na Oyo ya rasu

Gwamna Makinde ya ce tabbas al’ummar Musulmi za su yi kewar marigayin musamman irin gudunmawa da ya bayar, cewar Daily Post.

Kara karanta wannan

Gwamna Uba Sani ya ɗauki wasu muhimman matakai masu kyau kan jefa wa Musulmi bam a Tudun Biri

Har ila yau, dan tsohon Alaafin na Oyo, Abdulatai Adeyemi ya riga mu gidan gaskiya bayan fama da cutar sukari a jihar.

Marigayin wanda aka fi sani da ‘D-Gov’ ya rasu ne a asibitin Jami’ar Ibadan da ke jihar Osun da safiyar Juma’a 8 ga watan Disamba.

Imam Sa’id ya rasu a Gombe

A wani labarin, Allah ya karbi rasuwar babban limamin masallacin Izalah da ke Abuja Low-Coast a cikin garin Gombe.

Marigayin mai suna Imam Sa’id Abubakar ya rasu ne bayan fama da jinya na tsawon lokaci a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.