Rudani Yayin Da ’Yan Bindiga Su Ka Hallaka Babban Mai Sarautar Gargajiya da Su Ka Yi Garkuwa da Shi

Rudani Yayin Da ’Yan Bindiga Su Ka Hallaka Babban Mai Sarautar Gargajiya da Su Ka Yi Garkuwa da Shi

  • Bayan ‘yan bindiga sun sace mai sarautar gargajiya a yankin Otulu a jihar Imo, daga bisani an tsinci gawarsa a bakin hanya
  • Marigayin mai suna Eze Joe Ochulor an yi garkuwa da shi ne a ranar Asabar 25 ga watan Nuwamba
  • Kakakin rundunar ‘yan sanda a jihar, Henry Okoye ya tabbatar da kisan mai sarautar inda ya ce za su kama wadanda su ka aikata hakan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Imo – ‘Yan bindiga sun hallaka mai sarautar gargajiya a yankin Otulu a karamar hukumar Ezinihite Mbaise a jihar Imo.

Marigayin mai suna Eze Joe Ochulor an yi garkuwa da shi ne a ranar Asabar 25 ga watan Nuwamba, cewar The Sun.

Kara karanta wannan

Ku kara hakuri, Tinubu na da shirin ciyar da kasar nan gaba, shawarin minista ga 'yan Najeriya

'Yan bindiga sun hallaka mai sarautar gargajiya da su ka yi garkuwa da shi
Maharan sun harbe mai sarautar gargajiyar ne a jiya Asabar a Imo. Hoto: Hope Uzodinma.
Asali: Twitter

Yaushe aka hallaka mai sarautar?

Wata majiya ta tabbatar wa Punch cewa an tsinci gawar marigayin a bakin hanya a wani kauye da ke karamar hukumar Mbaise a ranar Asabar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyar ta ce:

“An hallaka mai sarautar gargajiya a yankin Otulu a karamar hukumar Ezinihite Mbaise a jihar Imo.
“An tsinci gawar mamacin a bakin hanya a karamar hukumar Mbutu a ranar Asabar da dare bayan sace shi da safiyar ranar.”

Mutanen yankin sun shiga tashin hankali saboda rashin sanin abin da ka iya biyo baya a yankin, cewar Chronicle.

Martanin 'yan sanda a kan kisan

Kakakin rundunar ‘yan sanda a jihar, Henry Okoye ya tabbatar da kisan mai sarautar inda ya ce za su kama wadanda su ka aikata hakan.

Ya ce kwamishinan ‘yan sanda a jihar ya umarci jami’an tsaro su bazama don binciko wadanda su ka aikata wannan danyen aiki.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun bindige shugaban PDP har lahira a gaban idon matarsa, an fadi wacce ake zargi

Wannan na zuwa ne bayan hallaka wani shugaban jam’iyyar PDP da wasu ‘yan bindiga su ka yi a jihar.

Maharan sun bindige Chiedoziem Anyanwu a gaban idon matarsa bayan sun bukaci ganinsa.

‘Yan bindiga sun hallaka shugaban PDP

A wani labarin, wasu ‘yan bindiga sun bindige Chiedoziem Anyanwu a gaban idon matarsa bayan sun bukaci ganinsa.

Marigayin shi ne shugaban jam’iyyar PDP a yankin Ife/Akpodim/Chokoneze da ke karamar hukumar Ezinihitte Mbaise a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.