“Na Rigada Na Siya Katifu da Gadaje”: Shahararren Dan Majalisa Aai Aurar da Yan Mata 100

“Na Rigada Na Siya Katifu da Gadaje”: Shahararren Dan Majalisa Aai Aurar da Yan Mata 100

  • Wani dan majalisar tarayya, Sani Yakubu Noma, ya bayyana aniyarsa na aurar da yan mata marayu 100 a jihar Kebbi
  • Dan majalisar ya bayyana cewa shirin auren na daya daga cikin gudunmawar da yake bayarwa wajenkula jin dadin marayu a mazabar sa
  • Noma ya ce za a daura auren ne a fadar mai martaba Sarkin Argungu, Alhaji Sama’ila Muhammad Mera a ranar Asabar 25 ga watan Nuwamba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Jihar Kebbi - Wani dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Argungu/Augie ta jihar Kebbi a majalisar wakilai, Sani Yakubu Noma, ya ce ya kammala duk wasu shirye-shirye don aurar da yan mata marayu su 100.

Kara karanta wannan

Miji ya zargi surukinsa hakimi, basarake a Kano da kashe masa aure tare da yunkurin tozarta shi

Da yake magana da manema labarai a mahaifarsa ta Argungu da ke jihar Kebbi, dan majalisar ya ce shirin yi wa yan matan auren gata yana daga cikin gudunmawarsa na kula da jin dadin marayu a mazabarsa.

Za a daura auren yan mata 100 a jihar Kebbi
Dan Majalisar Tarayya Zai Yi Wa Yan Mata Marayu 100 Auren Gata a Jihar Arewa Hoto: Anadolu. Hoton bai da alaka da labarin
Asali: Getty Images

Za a daura auren yan mata 100 a fadar Sarkin Argungu

Ya ce za a yi taron daurin auren ne a fadar sarkin Argungu, Mai martaba Alhaji Sama’ila Muhammad Mera a ranar Asabar, jaridar Daily Trust ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaridar Daily Post ta nakalto Yakubu Noma yana cewa:

"An kafa wani kwamiti domin ganin aiwatar da taron cikin nasara. Wadanda aka zaba za a yi wa auren gatan an zabo su ne daga kananan hukumomi biyu da nake wakilta a majalisar dokokin tarayya.
"Tuni na rigada na siyawawadanda suka ci gajiyar shirin kayan gadaje, katifu, kayan daki masu muhimmanci da sauran abubuwan bukata a gidan aure."

Kara karanta wannan

Dalilai 4 da suka sa Anyanwu na PDP ya fadi zaben gwamnan Imo na 2023

Dan majalisa ya aurar da marayu

A wani labari makamancin wannan, Legit Hausa ta kawo a baya cewa dan majalisa mai wakiltan mazabar Gusau/Tsafe a majalisar wakilai ta kasa, Kabiru Ahmadu Maipalace, ya dauki nauyin auren wasu yan mata marayu tara, karkashin shirinsa na kula da jin dadin mata, marayu da marasa gata.

Da yake gabatar da kayan daki da sauransu ga amaren a garin Gusau, babban birnin jihar Zamfara, a ranar Laraba, 15 ga watan Nuwamba, Maipalace ya ce ya yi hakan ne don cika alkawarin zabe da ya daukarwa al'umma.

Maipalace wanda ya samu wakilcin sakatarensa, Mustafa Hassan a wajen taron, ya bayyana cewa wannan abu da ya yi yana daga cikin shirinsa na tallafawa marasa gata karkashin kwamitinsa kan mata, marayu da marasa gata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng