Yan Bindiga Sun Kai Farmaki a Gona, Sun Yi Awon Gaba da Matan Aure 8

Yan Bindiga Sun Kai Farmaki a Gona, Sun Yi Awon Gaba da Matan Aure 8

  • Wasu matan aure sun faɗa hannun ƴan bindiga lokacin da su ke tsaka da gudanar da aikin gona a Abuja
  • Miyagun ƴan bindigan sun yi awon gaba da matan su takwas a ƙauyen Gwombe cikin ƙaramar hukumar Kuje
  • Sace matan auren na zuwa ne bayan ƴan bindiga sun yi awon gaba da mahaifin mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Kwali a Abuja

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ƴan bindiga sun yi awon gaba da matan aure takwas a wata gona da ke ƙauyen Gwombe a masarautar Gwargwada cikin ƙaramar hukumar Kuje a birnin tarayya Abuja.

Sace matan dai na zuwa ne kimanin sa'o'i 48 da ƴan bindiga suka yi garkuwa da mahaifin mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Kwali, tare da wasu mutum shida a ƙauyen Yewuti.

Kara karanta wannan

An kai farmaki hedikwatar rundunar yan sandan jihar Adamawa, bayanai sun fito

Yan bindiga sun sace mata a Abuja
Yan bindiga sun sace matan aure 8 a Abuja Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

Wani mazaunin Gwargwada mai suna Usman Yakubu ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 5:00 na yammacin ranar Litinin, 20 ga watan Nuwamba, cewar rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce matan suna girbin iri na benni ne a lokacin da ƴan bindigar ɗauke da bindigu ƙirar AK-47 suka kewaye su.

An tabbatar da aukuwar harin

Wani basarake daga wani ƙauye a masarautar, wanda ya gwammace a sakaya sunansa, ya tabbatar da sace mutanen, yana mai cewa:

“Haƙiƙa, huɗu daga cikin matan ƴan gida daya ne."

Ya ƙara da cewa:

"Ina zargin waɗannan ƴan bindiga da suka yi garkuwa da matanmu na daga cikin waɗanda suka tsere daga ƙauyen Kabbi da ke makwabtaka da su da ke yawo a cikin daji bayan da ƴan sakai na Miyetti Allah suka kashe wasu daga cikinsu a ƙarshen mako."

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai sabon hari a Abuja, sun sungume mahaifin babban dan siyasa da wasu mutum 6

Babu wani martani daga kakakin rundunar ƴan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Adeh Josephine, kan lamarin.

Ƴan Bindiga Sun Sace Matar Dagaci

A wani labarin kuma, wasu miyagun ƴan bindiga sun kai hari a ƙauyen Ruwandorawa cikin ƙaramar hukumar Maru ta jihar Zamfara.

Ƴan bindigan a yayin harin sun halaka ɗan sanda ɗaya tare da yin awon gaba da matar dagacin ƙauyen da wasu mutum 15

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng