Tsaro: Amurka Ta Gargadi Yan Kasarta da Su Guji Manyan Otel a Najeriya

Tsaro: Amurka Ta Gargadi Yan Kasarta da Su Guji Manyan Otel a Najeriya

  • Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya nuna fargaba kan yiwuwar tabarbarewar tsaro a kwanaki masu zuwa
  • Wannan sanarwar na kunshe ne a bayanin shawarari da ofishin jakadancin Amurka ya fitar a ranar Juma'a, 3 ga Nuwamba
  • An gargadi Amurkawa a Najeriya da su nisanci ottel-otel a garuruwan wasu manyan biranen kasar

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Amurka ta yi gagarumin gargadi ga yan kasarta da ke Najeriya, inda ta sanar da su "gagarumin barazana" da ke tattare da wasu manyan otel-otel a manyan biranen kasar.

An saki wannan gargadi ne a matsayin karin bayani na gaggawa ga yan kasar Amurka a ranar Juma'a, 3 ga Nuwamba.

Amurka ta gargadi yan kasarta da ke Najeriya kan lamarin tsaro
Tsaro: Amurka Ta Gargadi Yan Kasarta da Su Guji Manyan Otel a Najeriya Hoto: Joshua Lott
Asali: Getty Images

Sanarwar ta bayyana cewa hukumomin tsaron Najeriya suna tsaye kan lamarin domin dakile barazanar.

Kara karanta wannan

Kotun daukaka kara ta yanke hukunci kan makomar zaben sabon sanatan APC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bukaci yan kasar Amurka da su yi taka-tsan-tsan a lokacin da suka yi masauki a manyan otel-otel, su kula da muhallinsu, su zamo masu kankan da kai, sannan su yi bitar shawarar tafiye-tafiye a Najeriya kafin zabar masaukinsu.

Sanarwar ya zo kamar haka:

"Gwamnatin Amurka na sane da sahihan bayanai da ke nuna cewa akwai babbar barazana ga manyan otel-otel a manyan biranen Najeriya.
“Hukumomin tsaron Najeriya na aiki tukuru domin dakile wannan barazana.
"Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta shawarci yan Amurka da su yi la'akari da wannan bayanin yayin da suke shirin yin masauki ko ziyartar manyan otel-otel a Najeriya."

Sanarwar na kuma dauke da bayanan yadda za a tuntubi ofishin jakadancin Amurka a Abuja da ofishin jakadancin na Lagas koda wani dan Amurka zai bukaci taimako.

Kara karanta wannan

Zaben Bayelsa: Tashin hankali yayin da yan daba suka farmaki yan PDP, an kashe 1, wasu sun jikkata

Amurka ta gargadi yan kasarta a Najeriya

A wani labarin, mun kawo a baya cewa gwamnatin Amurka ta gargadi al'ummar kasar da su kaucewa zuwa wasu yankunan Najeriya saboda laifukan da suka shafi ayyukan ta’addanci, tashe tashen hankula da garkuwa da mutane.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta rahoto, Amurka ta yi gargadin ne a cikin wata sabuwar sanarwa da ta fitar kan shawarwarin tafiye-tafiye.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng