Jerin Sunaye: Najeriya, Isra'ila Da Sauran Kasashen Da Amurka Ba Ta Da Jakadu Da Kuma Dalili

Jerin Sunaye: Najeriya, Isra'ila Da Sauran Kasashen Da Amurka Ba Ta Da Jakadu Da Kuma Dalili

  • Amurka ta tabbatar da cewa akwai kasashe akalla 31 a fadin duniya da ba ta tura jakadunta ba, cikin su har da Najeriya, Masar, Isra'ila
  • Matthew Miller, kakakin ma'aikatar harkokin kasashen waje na Amurka, ya sanar da hakan yana mai cewa har yanzu Amurka ba ta tantance wadanda za ta tura ba
  • Miller ya fadi hakan a kan gabar tallafin da Amurka ke ba Isra'ila, kasar da ke ci gaba da harba ababen fashewa a Gaza tun bayan harin Hamas na farko a ranar 7 ga watan Oktoba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Amurka - Gwamnatin kasar Amurka ta ce har yanzu ba ta da jakada a Najeriya, duk da irin ci gaban da aka samu na kawance a tsakanin kasashen biyu.

Kara karanta wannan

Tashin hankali yayin da walkiya ta kashe dalibai suna tsaka da buga kwalla a Anambra

Matthew Miller, mai magana da yawun ma'aikatar kula da harkokin kasashen waje na Amurka, da ke aiki karkashin sakataren Amurka na US 71s, Anthony Blinken, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a shafinsa na X (tsohuwar Twitter).

Kasashen da Amurka ba ta tura jakadu ba
Duba sunayen kasashen da Amurka ba ta da jakadu. Hoto: Joe Biden, Bola Tinubu
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar Miller, Amurka ba ta tura da jakadanta zuwa kasar Najeriya da wasu kasashe 30 ba, sakamakon jiran da ake yi majalisar dattijai ta kasar ta tantance sunayen wadanda aka gabatar mata domin zama jakadu.

Kasashe 31 da kasar Amurka ba ta tura jakadunta ba

Idan aka cire Najeriya, sauran kasashen da Amurka ba da ta jakada a ciki sun hada da:

  1. Lebanon
  2. Isra'ila
  3. Masar
  4. Azerbaijan
  5. Lithuania
  6. Haiti
  7. African Union
  8. Turkmenistan
  9. Albaniya
  10. Zimbabwe
  11. Barbados
  12. Peru
  13. Ecuador
  14. Cape Verde
  15. Laos
  16. Nijar
  17. Djibouti
  18. Malaysia
  19. Gabon
  20. Burundi
  21. Croatia
  22. Guatemala
  23. Laberiya
  24. Somaliya
  25. Bahamas
  26. Colombia
  27. Kambodiya
  28. Montenegro
  29. Timor-Leste
  30. Tsibirin Marshall

Kara karanta wannan

“Na sha kuka”: Yar Najeriya ta yada hirar da ta gani a wayar mijinta

Karanta maganar ta sa:

Alakar da ke tsakanin Isra'ila da Amurka

Rahotanni sun bayyana cewa Amurka na goyon bayan Isra'ila akan ruwan ababen fashewa da ta ke saukar wa garuruwan Zirin Gaza, tun bayan da Hamas ta kaddamar da hari kan Isra'ila a ranar 7 ga watan Oktoba.

Babban Malami Joshua Iginla, shugaba kuma wanda ya assasa majami'ar Champions Royal Assembly, ya bukaci shuwagabannin kasashen duniya da su kawo karshen wannan fada da ake yi tsakanin Isra'ila da Gaza, gudun kar ya koma yakin duniya na uku.

A cikin wani bidiyo da majami'ar ta wallafa a shafinta na YouTube, malamin ya ce ya hango "wani babban yaki da ke tunkaro duniya. Kamar wata annoba, ba wai ta cutar rashin lafiya ba, sai dai annoba ta bindigu"

Tsakanin Isra'ila da Falasdinu: "Netanyahu na son haddasa yakin duniya na uku", cewar tsohon minista

Kara karanta wannan

‘'Gwamnatin Tinubu za ta tsamo 'yan Najeriya miliyan 50 daga kangin talauci,’' Betta Edu

Jaridar Legit Hausa ta ruwaito maku cewa Farfesa Bolaji Akinyemi, tsohon ministan harkokin wajen Najeriya, ya yi zargin cewa Benjamin Netanyahu, firaministan ƙasar Isra’ila, yana yunkurin kawo yaƙin duniya na uku.

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, tsohon ministan ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na ARISE a ranar Talata 10 ga watan Oktoba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.