Wazirin Fika, Adamu Ya Riga Mu Gidan Gaskiya Ya Na da Shekaru 90
- Ana cikin makoki bayan rasuwar Shahararren dan siyasa kuma ma'aikacin gwamnati, Alhaji Adamu Fika
- Marigayin ya rasu ne a daren jiya Talata 24 ga watan Oktoba yayin da ya ke cikin jirgi a kan hanyar dawo wa Najeriya
- Fika ya rike mukamai da dama da su ka hada Sakataren Gwamnatin Tarayya da shugaban ma'aikatan Gwamnatin Tarayya da sauransu
Jihar Kaduna - Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Adamu Fika ya rasu ya na da shekaru 90 a duniya.
Marigayin wanda shi ne Wazirin Fika ya rasu a daren jiya Talata 24 ga watan Oktoba a cikin jirgi yayin da ake dawo da shi da daga Ingila.

Source: Facebook
Yaushe marigayin, Wazirin Fika ya rasu?
Danburan Fika, Alhaji Idris Adama Kukuri shi ya tabbatar wa Daily Trust labarin mutuwar a wata ganawa ta wayar tarho.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Har zuwa yanzu ba a sanar da lokacin jana'izar ba inda majiyarmu ta ce sai an tuntubi Sarkin Fika, Alhaji Muhammadu Abali.
Majiyar ta ce jirgin da ya dauko marigayin ya sauka a Kaduna inda ake tunanin binne shi a can ko kuma komawa da shi Fika da ke jihar Yobe.
Wasu mukamin marigayin, Wazirin Fika ya rike?
Fika, kafin rasuwarshi ya rike mukamai da dama a gwamnati da samun lambar yabo masu tarin gaske, Leadership ta tattaro.
Fika kafin rasuwarshi, ya rike mukamin sakataren din-din-din a ma'aikatun Gwamnatin Tarayya da dama da su ka hada da ma'aikatar Kasuwanci da Sadarwa da kuma ta harkokin cikin gida.
Za a yi sallar jana'izarsa a masallacin Sultan Bello da ke birnin Kaduna a yau Laraba 25 ga watan Oktoba dai misalin karfe 4:00 na yamma.
Sabon kwamishina a jihar Borno ya riga mu gidan gaskiya
A wani labarin, sabon kwamishina a jihar Borno, injiniya Ibrahim Idris Garba ya riga mu gidan gaskiya a gidansa da ke Maiduguri babban birnin jihar.
Marigayin ya rasu ne da safiyar ranar Asabar 21 ga watan Oktoba a rukunin gidajen 777 a birnin Maiduguri da ke jihar Borno.
Rasuwar tashi na zuwa ne kwanaki kadan bayan Gwamna Babagana Zulum ya nada shi kwamishinan ayyuka da gyararraki da sake matsuguni a jihar.
Asali: Legit.ng

