Manya-Manyan Malaman Musulunci 5 da Su Ka Halarci Walimar Auren Gata a Kano
- Gwamnatin Kano ta aurar da mutane 1, 800 kuma ta gayyaci shehun malamai zuwa bikin auren da aka yi a gidan gwamnati
- An kira malamai daga bangarori da kungiyoyi dabam-dabam, wasu sun halarta yayin da wasu su ka aiko da wakilcinsu a taron
- Jagororin JIBWIS irinsu Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir da Muhammad Kabir Gombe sun halarci walimar da aka shirya
Kano - A ranar Juma’a, 13 ga watan Oktoba 2023, gwamnatin jihar Kano ta gudanar da auren gata a karkashin hukumar HISBAH.
Malaman addini sun halarci bikin da aka shiryawa ma’auratan bayan an daure auren a jiya.
An yi walimar ne a wata farfajiya da ke cikin gidan gwamnatin jihar Kano domin taya wadanda su ka yi auren murna da farin ciki.

Asali: Facebook
A rahoton nan, mun kawo jerin sunayen malamai da su ka halarci walimar, a ciki har da Bishof Isaac Idahosa wanda jigo ne a NNPP.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Idahosa wanda shi ne abokin Rabiu Musa Kwankwaso a karkashin jam’iyyar NNPP a zaben shugaban kasa na 2023, babban fasto ne.
1. Aminu Ibrahim Daurawa
A matsyinsa na shugaban hukumar HISBAH, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya sake jagorantar auren gatan da aka shirya a jiya.
2. Sani Yahaya Jingir
Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir ya halarci walimar, har ya gabatar da jawabi. A zaben 2023, ya bada shawarar a zabi NNPP a Kano.
3. Muhammad Kabir Gombe
Sakataren kungiyar JIBWIS na kasa, Muhammad Kabir Haruna Gombe ya je wajen walimar, ya kuma samu wuri a sahun gaba-gaba.
4. Aliyu Rasheed Makarfi
Ustaz Aliyu Rasheed Makarfi ya na cikin wadanda su ka tofawa taron albarka. Malamin ya yi suna wajen yin wa’azi a kan rayuwa da mu’amala.
5. Sani Shariff Bichi
Sheikh Sani Shariff Bichi wani shahararren malami ne da Legit ta hanga a wajen, shi ne shugaban majalisar malaman Kano na reshen Izalar-Jos.

Kara karanta wannan
Imam Ibrahim Kashim: Dan Jigon PDP Dan Shekara 24 Da Tinubu Ya Nada Shugaban FERMA
Shawarar Rabiu Musa Kwankwaso
Rabiu Musa Kwankwaso ya yi kira ga ma'uratan da su guji leka wayoyin juna domin hakan shi ne babban abin da ya ke raba aure a zamanin nan.
An rahoto Kwankwaso ya na yabawa yadda Abba Kabir Yusuf ya farfado da manufofin gwamnatin Kwankwasiyya da ya kirkiro a Kano.
Asali: Legit.ng