Lagos: Rundunar Soji Ta Tono Bama-Bamai a Wurin da Bam Ya Tashi a Ikeja

Lagos: Rundunar Soji Ta Tono Bama-Bamai a Wurin da Bam Ya Tashi a Ikeja

  • Dakarun sojin Najeriya sun gano ƙarin bama-bamai da wurin da ababen fashewa suka tashi a Ikeja shekaru 21 da suka wuce
  • Babban hafsan sojojin ƙasa, Laftanar Janar Lagbaja ya kaddamar da atisayen sake tsaftace wurin ranar Talata a jihar Legas
  • A watan Janairu, 2002 ne aka sami tashin Bama-Bamai a sansanin soji da ke Ikeja, lamarin da ya halaka aƙalla rayuka 1,100

Ikeja, jihar Legas - Hukumar sojin Najeriya ta ƙara tono ababen fashewa a wurin da Bam ya tashi shekaru 21 da watanni tara da suka gabata a Ikeja, babban birnin jihar Legas.

Hukumar sojin ƙasa ta Najerriya ce ta tabbatar da haka a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta naanhajar X wanda aka fi sani da Twitter a kwanakin baya.

Shugaban rundunar sojin ƙasan Najeriya, Manjo Janar Lagbaja.
Lagos: Rundunar Soji Ta Tono Bama-Bamai a Wurin da Bam Ya Tashi a Ikeja Hoto: Nigerian Army
Asali: Twitter

Taƙaitaccen bayani kan abinda ya faru a 2002

Kara karanta wannan

Jarabawar NECO 2023: Jerin Jihohin Da Suka Samu Sakamako Mai Kyau Da Wadanda Suka Samu Akasin Haka

Tashin bama-baman wanda ya auku ranar 27 ga watan Janairu, 2002 a sansanin sojoji da ke Ikeja, ana kyautata zaton ya halaka mutane aƙalla 1,100 yayin da wasu sama da 20,000 suka rasa mahallansu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bayan haka tashin Bama-baman ya jikkata dubbannin mutane tare da jefa wasu da dama cikin halin kaƙanikayi.

An ce Bama-bamai da wasu ababen fashewa sun tashi ne bisa kuskure a cikin sashin ajiye makamai na barikin sojoji sama da shekaru 21 da suka wuce.

Fashewar wadda ta yi kara kusan sau bakwai, cikin kwanaki biyu, ta yi sanadin lalata dukiyoyi a yankin da kewaye. Lamarin da ba a taba ganin irinsa ba a tarihi.

Rundunar soji ta fara aikin tsaftace wurin da abun ya faru

Da yake jawabi a Legas ranar Talata yayin kaddamar da shirin tsaftace wurin, babban Hafsan Sojojin ƙasa (COAS), Laftanar-Janar Tajudeen Lagbaja, ya ce a karshe rundunar ta soma aikin kwashe abinda ya rage.

Kara karanta wannan

Malamin Makaranta Ya Ɗebo Ruwan Dafa Kansa Bayan Ya Zane Ɗaliba Mace a Abuja

COAS ya bayyana cewa rundunar soji ta fara jigilar sauran bama-bamai da ababen fashewar da ba su fashe ba a wancan lokacin zuwa daya daga cikin sansanonin ta da ke Ajilete, jihar Ogun.

Ya ce aikin shara da tsaftace wurin na farko da aka yi a shekarar 2002 ya ƙara tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a yankin Ikeja da kewaye.

Sojoji sun ƙara tono bama-bamai a wurin

Lagbaja ya ƙara da cewa sun gano wasu bama-bamai da ba su fashe ba a wurin da ibtila'in ya faru kuma hakan ne ya nuna akwai buƙatar sake tsaftace wurin a yanzu.

"Ina ƙara tabbatar wa yan Najeriya musamman mazauna Legas da Ogun cewa za a gudanar da wannan aiki cikin ƙwarewa da kuma taka tsantsan da bin matakan da ya dace."

Yan Bindiga Sun Halaka Basarake, Sun Yi Awon Gaba da Mutane da Yawa a Niger

A wani rahoton kuma Yan bindiga sun yi ajalin Basarake, sun tattara jama'a sun yi awon gaba da su a ƙauyukan jihar Neja ranar Talata da daddare.

Rahotanani daga mazauna yankin sun nuna cewa maharan sun haɗa harda mata sun yi garkuwa da su, sun sace dabbobi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262