Kotu Ta Yankewa Wadanda Suka Sace Mike Ozekhome Shekaru 20 a Kurkuku

Kotu Ta Yankewa Wadanda Suka Sace Mike Ozekhome Shekaru 20 a Kurkuku

  • Kotu ta yankewa wasu masu garkuwa da mutane biyu da suka sace babban lauyan Najeriya, Mike Ozekhome, hukuncin shekaru 20 a gidan yari
  • Hukuncin na zuwa ne shekaru 10 bayan masu laifin sun sace Ozekhome a Iruekpen a hanyarsa ta zuwa Iviukwe a Agenebode, Edo
  • Sai dai kuma, Mai shari'a Binta Nyako, ta sallama tare da wanke wasu biyu da ake tuhuma da laifin ta’addanci

FCT, Abuja - An yankewa Kelvin Ezeigbe da Frank Azuekor, biyu daga cikin mutane hudu da ake zargi da garkuwa da Mike Ozekhome, SAN, hukuncin shekaru 20 a gidan yari.

Mai shari'a Binta Nyako ta babbar kotun tarayya, Abuja, ce ta yanke hukuncin a ranar Juma'a, 6 ga watan Oktoba, jaridar The Nation ta rahoto.

Kotu ta yankewa wadanda suka sace Mike Ozekhome San hukunci
Kotu Ta Yankewa Wadanda Suka Sace Mike Ozekhome Shekaru 20 a Kurkuku Hoto: Mike Ozekhome San
Asali: Facebook

Mai shari'a Nyko ta riki cewa hukuncin zai fara aiki ne daga ranar da aka kama su.

Kara karanta wannan

Sunan Ministan Buhari Ya Fito Wajen Shari’a da Diezani Alison-Madueke a Kotu

Kotu ta wanke wasu mutum biyu

Haka kuma, mai shari'ar ta sallama tare da wanke sauran mutum biyu da ake zargi, Michael Omonigho da Momoh Haruna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An fara gurfanar da wadanda ake zargin ne a gaban mai shari’a Adeniyi Ademola na babbar kotun tarayya, a ranar 9 ga watan Yunin 2014, bisa tuhume-tuhume 13 da suka hada da hada baki, fashi da makami, garkuwa da mutane da kuma ayyukan ta’addanci.

An dai zargi Kelvin Ezeigbe, Frank Azuekor, Michael Omonigho da Momoh Haruna, da yin garkuwa da Ozekhome a Iruekpen akan hanyarsa ta zuwa Iviukwe a Agenebode, Edo.

An yi zargin cewa sun yi garkuwa da Ozekhome a Iruekpen akan hanyarsa ta zuwa Iviukwe a Agenebode, Edo, a ranar 23 ga Agusta, 2013.

Ozedkhome ya shafe kimanin makonni uku a tsare kafin aka sake shi bayan biyan naira miliyan 28 a matsayin kudin fansarsa.

Kara karanta wannan

Za a Tsare Mawaka, Naira Marley da Sam Larry na Kwana 21 a Kan Mutuwar Mohbad

Sanata Zam: Iyayena na cikin kuncin rayuwa a sansanin 'yan gudun hijira a Benue

A wani labarin, wani Sanata a jihar Benue, Titus Zam ya bayyana cewa iyayensa na cikin kunci a sansanin 'yan gudun hijira a jihar.

Sanatan wanda ke wakiltar Arewa maso Yammacin jihar ya ce hakan ya faru sanadiyyar hare-haren 'yan bindiga a shekarar 2022, Legit ta tattaro.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng