Balarabe Abbas Lawal: Tarihin Wanda Zai Canji El-Rufai a Kujerar Ministan Kaduna

Balarabe Abbas Lawal: Tarihin Wanda Zai Canji El-Rufai a Kujerar Ministan Kaduna

  • Balarabe Abbas-Lawal ya kama hanyar zama sabon Minista a gwamnatin Bola Ahmed Tinubu
  • Sakataren na gwamnatin jihar Kaduna zai maye gurbin mutuminsa wanda majalisa ta ki tantacewa
  • Malam Lawal ya yi sama da shekaru takwas ya na kan kujerar sakataren gwamnati a jihar Kaduna

Abuja - Bola Ahmed Tinubu ya zabi Balarabe Abbas-Lawal domin ya zama wanda zai wakilci jihar Kaduna a majalisar zartarwa watau FEC.

Legit.ng Hausa ta tattaro gajeren bayani game da tarihin sakataren gwamnatin Kadunan.

Balarabe Abbas Lawal
Nasir El-Rufai da Balarabe Abbas Lawal Hoto: @GovKaduna
Source: Twitter

Wanene Balarabe Abbas Lawal?

1. An haifi Abbas Lawal ne a Fubrairun 1958, yanzu haka ya na da shekaru 65 a duniya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

2. Tsakanin 1964 da 1970 ya halarci makarantar firamare ta gwamnati a Kofar Kuyambana a Zariya.

Kara karanta wannan

To fah: Inuwar lema ta dauki dumi, tsohon gwamnan Kaduna ya fice daga PDP

3. A shekarar 1971 ya shiga makarantar Baewa College, hakan ya ba shi damar haduwa da Nasir El-Rufai.

4. Ministan na gobe ya yi sharar fage a makarantar da ake kira Katsina College of Arts, Science and Technology.

5. Zuwa 1981, sai ga Balarabe Abbas Lawal ya samu shaidar digiri a ilmin kimiyyar siyasa daga jami’ar ABU Zariya.

6. Baya ga digirin farko, ya sake komawa jami’ar domin yin digiri na biyu watau M.Sc duk a ilmin siyasa.

7. Lawal ya yi kwas iri-iri kama GMC, ASCON, MTC, CFED, IP3, IVLP a Legas, Amurka, Ingila, Kanada da sauransu.

8. Karatun da ya samu a Thames Valley College da jami’o’i irinsu Harvard sun taimaka masa wajen zama malami.

9. A baya ya yi aiki da kamfanonin ASCON da NEPA da gwamnatin tarayya ta rusa su a shekarun baya.

10. A lokuta dabam-dabam, Malam Balarabe Abbas Lawal ya yi aiki da ministocin ilmi da na tsaro a Najeriya.

11. Yayin da Nasir El-Rufai yake ministan harkokin birnin Abuja, shi ne shugaban ma’aikatan fadarsa.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu, Mataimakin Gwamna da Sanata Sun Dira Kotun Zaɓe Kan Nasarar Gwamnan APC

Balarabe Abbas Lawal a gwamnatin Kaduna

12. Lawal ya jagoranci aikin mika mulki a gwamnatin jihar Kaduna bayan zabukan 2015 da na 2023.

13. A sakamakon nasarar El-Rufai a zaben 2015, sai ya dauko tsohon hadiminsa domin zama sakataren gwamnati.

14. Bayan tazarce da APC ta yi a 2019, Lawan ya cigaba da zama a kan kujerar sakataren gwamnatin Kaduna.

15. Ko da Uba Sani ya karbi mulki, ya bar Abbas-Lawal a kujerarsa domin ganin ya sa kan aiki a jihar Kaduna.

Nasir El-Rufai bai dace ba

Idan Balarabe Abbas Lawal ya samu amincewar majalisar dattawa, zai rike kujerar da mai gidansa, Malam Nasir El-Rufai bai iya komawa kai ba.

Ku na da labarin abubuwan da su ka jawo 'yan majalisa su ka ki amincewa tsohon gwamnan Kaduna ya zama minista a gwamnatin Bola Tinubu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng