Bikin Murna Ya Barke a Gabon Yayin da Sojoji Suka Karbe Mulki Daga Shugaban Kasa Ali Bongo, Hotuna Sun Bayyana

Bikin Murna Ya Barke a Gabon Yayin da Sojoji Suka Karbe Mulki Daga Shugaban Kasa Ali Bongo, Hotuna Sun Bayyana

  • Jami'an sojoji a Gabon sun bayyana a talbijin din kasar a ranar Laraba don ayyana cewa sun karbe mulkin kasar
  • Wannan al'amari ya haifar da bikin murna sannan mutane sun fito titunan babban birnin kasar don nuna farin ciki
  • Sanarwar na zuwa ne a daidai lokacin da Shugaban kasa Ali Bongo Ondimba ya lashe zaben kasar, wanda hakan ya ba iyalinsa damar ci gaba da mulkin kasar

Libreville, Gabon - Masu goyon bayan kwace mulki da sojoji suka yi a kasar Gabon da dama sun yi tururuwar fitowa kan titinunan unguwanninsu.

Hotunan da Legit.ng ta gano sun nuna al'ummar garo suna jinjinawa dakarun rundunar tsaro a yankin Plein Ciel da ke Libreville, babban birnin kasar Gabon.

Rundunar sojojin kasar Gabon ta sanar da hambarar da gwamnatin shugaban kasa Ali Bongo.

Kara karanta wannan

Cire Tallafi: Kwastomomi Sun Rage Zuwa Gida Karuwai a Kano, Gidan Magajiya Ya Dauki Zafi

Yan farar hula na murnar juyin mulki da sojoji suka yi a kasar Gabon
Bikin Murna Ya Barke a Gabon Yayin da Sojoji Suka Karbe Mulki Daga Shugaban Kasa Ali Bongo, Hotuna Sun Bayyana Hoto: Nelly Ada-Ndiuche Izuogu Agwu
Asali: Facebook

Juyin mulkin Gabon: Yan farar hula na murna

Al Jazeera ta watso shirin kai tsaye kan halin da ake ciki a Libreville kan rikicin Gabon a ranar Laraba, 30 ga watan Agusta.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Iyalan Bongo ne ke mulkin kasar da ke yammacin Afirka tun bayan samun yancin kai daga kasar Faransa a shekarar 1960.

Wannan juyin mulkin babban koma-baya ne ga Najeriya, Shugaban kasa Bola Tinubu, kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), da kawayenta da ke fafutukar ganin sun karbe mulki daga hannun masu mulkin soja a Jamhuriyar Nijar.

Sojoji Sun Kifar Da Gwamnatin Shugaba Ali Bongo Na Kasar Gabon

Da farko mun ji cewa sojoji sun bayar da sanarwa na kifar da gwamnatin Shugaba Ali Bongo a kasar Gabon, bayan ya lashe zaben da ya gudanara a kasar a ranar Asabar, 26 ga watan Agusta.

Kara karanta wannan

Rikicin Jamhuriyar Nijar: Jerin Manyan Abubuwa 5 Da Suka Faru Cikin Makon Nan

Bongo, wanda ya hau karagar mulki bayan mutuwar mahaifinsa a shekarar 2009, ya lashe zabe a karo na uku.

Sojojin Nijar sun datse samar da wuta da ruwa zuwa ofishin jakadancin Faransa

A wani labari na daban, mun ji cewa sojojin juyin mulki a Nijar sun bayar da umurnin datse hamyar samar da wuta da ruwa zuwa ofishin jakadancin kasar Faransa da ke kasar.

Sojojin sun kuma bayar da umurnin dakatar da kai abinci zuwa ofishin jakadancin da ke Zinder.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng