ECOWAS Ta Buƙaci Sojojin Nijar Su Mika Mulki, Su Koma Su Ci Gaba Da Tsaron Ƙasarsu

ECOWAS Ta Buƙaci Sojojin Nijar Su Mika Mulki, Su Koma Su Ci Gaba Da Tsaron Ƙasarsu

  • Wasu 'yan ta'adda ɗauke da muggan makamai sun halaka sojojin Nijar a wani hari da suka kai mu su
  • Kungiyar ECOWAS ta nuna rashin jin dadinta bisa faruwar wannan mummunan lamari
  • Sai dai ECOWAS ta yi kira ga sojojin da su mayar da mulki hannun Mohamed Bazoum domin su mayar da hankali kan tsaron ƙasa

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Kungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), ta yi martani dangane da kashe sojojin jamhuriyar Nijar da wasu 'yan ta'adda suka yi.

A wani saƙo da aka wallafa a shafin ECOWAS na Twitter, ƙungiyar ta yi Allah wadai da harin da 'yan ta'addan suka kai a kan sojojin na Nijar.

Kungiyar ECOWAS ta yi Allah wadai da harin 'yan ta'adda kan sojojin Nijar
ECOWAS ta nuna rashin jin daɗinta kan harin da 'yan ta'adda suka kai wa sojojin jamhuriyar Nijar. Hoto: @BashirAhmad
Asali: Twitter

ECOWAS ta buƙaci sojojin Nijar su mayarwa Bazoum mulki

Bayan Allah wadai da harin 'yan ta'addan kan sojojin jamhuriyar Nijar da ECOWAS ta yi, ta nemi sojojin su yi babban abinda ya dace.

Kara karanta wannan

Shugabannnin Rundunonin ECOWAS Za Su Yi Taro Dangane Da Umarnin Ɗamarar Yaƙi Da Sojojin Nijar Da Aka Ba Su

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

ECOWAS ta nemi sojojin su mayar da mulki hannun hamɓararren shugaban ƙasar ta Nijar Mohamed Bazoum da suka yi wa juyin mulki a baya.

ECOWAS ta kuma shawarci sojojin su koma bakin daga domin tsare ƙasar daga hare-haren 'yan ta'adda bayan mayar da mulkin hannun farar hula.

Fargabar yaƙi yayin da hafsoshin tsaron ECOWAS ke shirin yin taro

A baya Legit.ng ta yi rahoto kan taron da shugabannin rundunonin tsaron ƙasashen ECOWAS ke shirin yi a makon nan da muke ciki.

Shugabannin rundunonin tsaron na ECOWAS sun tsaida ranar Alhamis, 17 ga watan Agustan da muke ciki a matsayin ranar da za su taru domin tattauna yiwuwar amfani da ƙarfin soji kan jamhuriyar Nijar.

An bayyana cewa shugabannin tsaron ƙasashen ECOWAS 11 ne za su halarci taron da za a yi a Accra babban birnin ƙasar Ghana.

Kara karanta wannan

Abinda Sakataren Amurka Ya Faɗawa Tinubu Kan ECOWAS Dangane Da Juyin Mulkin Nijar

An samu rabuwar kai a majalisar ECOWAS

Legit.ng a baya ta yi rahoto kan rarrabuwar kawunan da aka samu tsakanin 'yan majalisun ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS) kan tura sojoji Nijar.

Wasu daga cikin 'yan majalisar ta ECOWAS sun amince da tura dakaru domin su karɓi mulki ta ƙarfi, a yayinda wasu kuma suka nuna ƙin amincewarsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng