Masu PhD 3: Matakin Karatun Mutanen da Tinubu Ya Zaba a Matsayin Ministocinsa

Masu PhD 3: Matakin Karatun Mutanen da Tinubu Ya Zaba a Matsayin Ministocinsa

A ranar Talata ne shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya mika jerin sunayen ministocinsa 28 ga majalisar dokokin kasar domin tantance su, kafin cikar wa’adin kwanaki 60 da dokar kasar ta kayyade.

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Rahotanni sun shaida cewa, an zabo wadanda aka nadan ne daga jihohi 25 na tarayyar kasar - ban da jihohi 11.

Wani binciken da TheCable Index ta yi ya nuna cewa mafi karancin matakin karatun wadanda aka zaba shine digiri na farko kuma mafi girma shi ne mai digirin digirgir.

Yayin da mutane 16 da Tinubu ya zaba ke da digiri biyu, tara daga cikin 28 din na da digirin farko, inda mutum uku kuwa ke da digirin digirgir.

Wadanda aka nada ministoci
Ministocin da Tinubu ke son aiki dasu | Hoto: channelstv.com
Source: UGC

Biyu daga cikin wadanda ke da digirin digirgir din ma sun yi aiki da samun gogewar da suka za su iya zama farfesoshi.

Kara karanta wannan

Kace-Nace Yayin Da 'Yan Najeriya Suka Soki Yadda Tinubu Ya Zabi Ministoci, Sun Bayyana Abin Da Ya Kamata

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Su waye ya kamata a nada kujerun minista?

A cewar sashe na 147(5) na kundin tsarin mulkin kasar, mutum ba zai cancanci kujerar minista ba har “sai dai idan ya cancanta a zabe shi a matsayin dan majalisar wakilai”.

Sashi na 65 (1) (a) na kundin tsarin mulkin kasar ya bayyana cewa mutum zai iya takarar majalisar wakilai ne idan ya samu ilimi har zuwa akalla matakin karantun satifiket ko makamancinsa.

Duk da cewa dukkan wadanda aka nada sun cancanta a bisa tanadin kundin tsarin mulkin kasar, a baya ‘yan majalisar sun bayyana ra’ayinsu game da mafi karancin matakin karatu.

A watan Janairun 2022, Femi Gbajabiamila, tsohon kakakin majalisar wakilai, ya ce akwai bukatar a yi wa kundin tsarin mulki kwaskwarima domin kara tsaurara cancantar matakin karatu a zaben ofishin majalisar dokokin kasar.

Majalisar wakilai, a watan Fabrairun 2022, ta fara aiwatar da shirin kara mafi karancin cancantar ilimi na zabe a matsayin gwamna, dan majalisar jiha da na tarayya, zuwa akalla “matakin digiri na jami’a ko makamancinsa”.

Kara karanta wannan

Hankula Sun Tashi Yayin Da 'Yan Bindiga Suka Bindige Wasu Dalibai A Shagon Aski, 'Yan Sanda Sun Yi Martani

Matakin karatun ministocin Tinubu

Lamba

Suna

Matakin karatu

1

Abubakar Momoh

Digiri na daya

2

Yusuf Maitama Tuggar

Digiri na biyu

3

Ahmad Dangiwa

Digiri na biyu

4

Hanatu Musawa

Digiri na biyu

5

Uche Nnaji

Digiri na daya

6

Betta Edu

Digirin digirgir

7

Doris Uzoka

Digiri na daya

8

David Umahi

Digiri na daya

9

Nyesom Wike

Digiri na biyu

10

Mohamed Badaru

Digiri na daya

11

Nasir El-Rufai

Digiri na biyu

12

Ekperikpe Ekpo

Digiri na biyu

13

Nkeiruka Onyejeocha

Digiri na biyu

14

Olubunmi Tunji-Ojo

Digiri na biyu

15

Stella Okotete

Digiri na biyu

16

Uju Ohanenye

Digiri na daya

17

Bello Mohammed Goronyo

Digiri na daya

18

Dele Alake

Digiri na biyu

19

Lateef Fagbemi

Digiri na biyu

20

Mohammed Idris

Digiri na biyu

21

Olawale Edun

Digiri na biyu

22

Adebayo Adelabu

Digiri na daya

23

Imaan Sulaiman-Ibrahim

Digiri na biyu

24

Ali Pate

Digirin digirgir

25

Joseph Utsev

Digirin digirgir

26

Abubakar Kyari

Digiri na dbiyu

27

John Enoh

Digiri na biyu

28

Sani Abubakar Danladi

Digiri na daya

Kara karanta wannan

Tashin Hankali: An Ƙara Samun Fashewa a Najeriya, Mutane Sama da 20 Sun Mutu

Abubuwa 5 da ya kamata ku sani game da zabebben ministan Tinubu da ya yi aiki da tsohon shugaba Jonathan

A bangarensa, Farfesa Mohammed Ali Pate wanda ɗan jihar Bauchi ne, ya samu damar shiga cikin jerin ministocin da Shugaba Tinubu zai naɗa cikin 'yan kwanakin nan.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio ne ya karanto sunayen mutane 28 da shugaban ƙasa ya aikawa majalisar domin a tantancesu.

Kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito, waɗannan wasu abubuwa ne guda 5 da ya kamata ku sani game da sabon ministan Tinubu, Farfesa Mohammed Ali Pate:

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng