Jerin Jihohin Da Suka Samar Da Ministoci 2 a Lokacin Mulkin Buhari

Jerin Jihohin Da Suka Samar Da Ministoci 2 a Lokacin Mulkin Buhari

Tsohon shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya nada ministoci 44 a lokacin mulkinsa na biyu a shekarar 2019.

Kamar yadda jaridar Premium Times ta rahoto, daga cikin ministoci 44 da aka nada, jihohi bakwai sun samu fiye da kujerar minista daya.

uhari ya nada ministoci 44 a mulkinsa
Jerin Jihohin Da Suka Samar Da Ministoci 2 a Lokacin Mulkin Buhari Hoto: Muhammadu Buhari/ Hon Chris Ngige/Babatunde Raji fashola/Ebele Chukwujekwu
Asali: Facebook

Bisa ga rahoton Vanguard, ga jerin sunayen ministocin, jihohi da kuma ayyukansu a kasa:

Jihar Anambra ta samu ministoci biyu

Chris Ngige – Jihar Anambra – Ministan kwadago da daukar ma'aikata

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Sharon Ikeazor – Jihar Anambra – Karamin ministan muhalli

Buhari ya nada ministoci 2 daga jihar Bauchi

Adamu Adamu — Jihar Bauchi – Ministan ilimi

Ambasada Maryam Katagum – Jihar Bauchi – Karamar ministar kasuwanci

Kara karanta wannan

Mutanen El-Rufai Sun Dawo Cikin Sababbin Kwamishonin Gwamna Uba Sani a Kaduna

An nada ministoci 2 daga jihar Edo

Osagie Ehanire — Jihar Edo – Ministan lafiya

Clement Ike – Jihar Edo — Karamin ministan kasafin kudi

Jihar Kaduna ta samar da ministoci 2

Zainab Ahmed – Jihar Kaduna – Ministar kudi

Muhammad Mahmood – Jihar Kaduna – Ministan muhalli

Ministoci 2 daga jihar Kano

Sabo Nanono – Jihar Kano – Ministan noma da raya karkara

Bashir Salihi Magashi – Jihar Kano - Ministan tsaro

Buhari ya nada yan asalin jihar Kwara minista

Lai Mohammed – Jihar Kwara – Ministan labarai da al'adu

Gbemisola Saraki – Jihar Kwara – Karamar ministar sufuri

Jihar Lagas ta samu ministoci 2

Babatunde Fashola – Jihar Lagos – Ministan ayyuka da gidaje

Adeleke Mamora – Jihar Lagos – Karamin ministan lafiya

Na hannun damar Buhari da suka samu aiki bayan karewar wa'adin mulkinsu

A wani labarin, mun ji cewa Lai Mohammed wanda ya rike Ministan yada labarai da al’adu na Najeriya a gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya samu aiki da wani kamfanin ketare mai suna Ballard Partners.

Kara karanta wannan

Daga Karshe, Hukumar DSS Ta Gurfanar da Dakataccen Gwamnan CBN a Kotu, Sabbin Bayanai Sun Fito

A wata sanarwa da Ballard Partners ya fitar a shafinsa na Twitter, an tabbatar da cewa Alhaji Lai Mohammed ya zama daya daga cikin abokan huldarsu.

Femi Adesina ya samu aiki bayan barin mulki

Hakazalika, tsohon kakakin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Femi Adesina, ya samu aiki kwanaki kadan bayan sauka daga mulki.

Adesina ya bayyana cewa zai fara aiki a matsayin mataimakin shugaban kamfanin jaridar Sun daga ranar 1 ga watan Satumba, 2023.

Adesina ya rike kambun shugaban marubutan jaridar TheSun kafin daga bisani tsohon shugaban ƙasa Buhari ya naɗa shi a matsayin mai magana da yawunsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng