Rundunar Sojin Sama Ta Kashe Yan Ta’addan ISWAP Masu Yawan Gaske a Jihar Borno

Rundunar Sojin Sama Ta Kashe Yan Ta’addan ISWAP Masu Yawan Gaske a Jihar Borno

  • Dakarun rundunar sojojin saman Najeriya sun yi gagarumin nasara a kan mayakan kungiyar ta'addanci da suka addabi yankin arewa maso gabas
  • Sojojin sun yi yayyafi wuta a kan mayakan ISWAP da dama a yankin Marte da ke jihar Borno
  • An kai farmakin ne bayan binciken sirri ya nuna akwai yan ta'adda masu yawan gaske a yankin

Borno - Dakarun rundunar sojojin saman Najeriya sun halaka mayakan kungiyar ta'addanci na ISWAP da dama a wani mummunan hari da suka kai masu ta sama a ranar Laraba, 5 ga watan Yuli.

Zagazola Makama ya rahoto cewa rundunar sojin saman ta yi wa mayakan yayyafin wuta ne a kusa da Marte, hedkwatar wata karamar hukuma a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

Jirgin sojojin Najeriya
Rundunar Sojin Sama Ta Kashe Yan Ta’addan ISWAP Masu Yawan Gaske a Jihar Borno Hoto: Daily Post
Asali: UGC

Dakarun Operation Hadin Kai sun ragargaji yan ISWAP ta sama

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: Shugaba Tinubu Ya Sa Labule da Shugaban APC Na Ƙasa da Sakatare a Villa

An kashe yan ta'addan ne a wani farmaki da rundunar sojin Operation Hadin Kai suka kai ta sama a Tumbum SHITTU.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kwararren masanin lamarin tsaro a yankin tafkin Chadi, Zagazola Makama, wanda ya bayyana haka a ranar Alhamis, 6 ga watan Yuli, ya ce an aiwatar da farmakin sojin ne bayan bincike ya nuna akwai tarin yan ta'addan a yankin.

Wata majiyar sirri da ta nemi a sakaya sunanta ta ce:

"An kai harin saman ne da nufin kawar da mabuyan yan ISWAP."

Gwamnatin Babagana Zulum ta sha alwashin daukar mummunan mataki a kan mayakan ISWAP

A wani labari na daban, gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum ya nuna bakin cikinsa a kisan gillar da mayakan ISWAP suka yi wa wasu manoma takwas a karamar hukumar Mafa ta jihar Borno.

Kara karanta wannan

Fashin Fadar Sarkin Minna: Bincike Ya Nuna Da Dan Gari Aka Ci Gari, An Tabbatar Da Mutuwar Dogarawa 2

An dai farmaki manoman ne garuruwan Shuwarin, Tomsu Ngamdu, Baram Karauwa da Muna a ranar Alhamis, yayin da suke tsaka da aiki a gonakinsu

Zulum wanda ya ziyarci Mafa, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

An kashe kasurgumin dan bindigan Zamfar, Dogo Gudali

A gefe guda, mun ji cewa kasurgumin shugaban yan bindiga, Dogo Gudali, wanda ya addabi al'umma musamman a jihar Zamfara ya kwanta dama

Gudali ya hadu da ajalinsa ne bayan wasu mambobin kungiyarsa na ta'addanci sun dana bam da nufin farmakar dakarun sojoji.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng