Dalibai 8 Da ’Yan Bindiga Suka Sace a Kaduna Sun Kubuta, Gwamna Ya Yaba da Kokarinsu

Dalibai 8 Da ’Yan Bindiga Suka Sace a Kaduna Sun Kubuta, Gwamna Ya Yaba da Kokarinsu

  • Wasu dalibai sun yi nasarar tserewa daga hannun ‘yan ta’addan da suka sace su a farkon watan nan na Afrilu da muke ciki
  • An ruwaito cewa, takwas daga cikin daliban ne suka tsere tare da neman taimakon da ya kai su ga isowa hannun jami’an tsaro
  • Gwamna El-Rufai na Kaduna ya yaba da irin kokarin da daliban suka yi na tsira daga hannun ‘yan ta’adda masu cutarwa

Jihar Kaduna - Dalibai takwas na makarantar gwamnati ta sakandare da ke Awon a jihar Kaduna da aka sace sun yi nasarar tserewa daga hannun ‘yan bindiga.

An sace daliban ne a ranar 3 ga watan Afrilu a yankin Awon na karamar hukumar Kachia ta jihar da ke Arewa maso Yammacin Najeriya, Daily Trust ta ruwaito

Kara karanta wannan

Jerin Matan Arewa Da Suka Ciri Tuta A Siyasar Najeriya Da Maza Suka Yi Kaka-Gida

A cewar majiyoyi, daliban sun yi nasarar tserewa ne daga kungurmin dajin da aka boye su wanda ke tsakanin jihar Kaduna da Neja a yankin.

Dalibai sun tsere daga hannun 'yan ta'adda a Kaduna
Jihar Kaduna da ke Arewa maso Yamma | Hoto: thenationonlineng.net
Asali: UGC

Yadda daliban suke tsere

An tattaro cewa, daliban mata sun yi tafiyar tazara kuma ta tsawon kwanaki kafin daga bisani suka gane inda suke, sai suka nemi taimakon a kawo su gida.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida a Kaduna, Samuel Aruwan ya fitar da sanarwar da ke tabbatar da kubutar wadannan daliban.

A sanarwar ta ranar Talata 18 Afirilu, 2023, Aruwan ya ce an sanar da gwamnatin jihar labarin kubutar daliban, wanda gwamna Malam Nasir El-Rufai na jihar ya umarci a gaggauta dauko su.

'Yan ta'adda na ci gaba da neman daliban

A cewarsa, yanzu haka ‘yan ta’addan na ta sintiri da binciken kwakwaf a cikin dajin don sake kama daliban da suka tseren, PM News ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Makarkashiyar Gwamnonin PDP Ta Jawo Rikicin Cikin Gidan Jam’iyya Zai Koma Sabo

Ya kara da cewa, takwasi daga cikinsu ne sojoji suka dauko, inda a halin yanzu suke karbar kulawar likitoci a asibiti.

Aruwan ya ce, gwamna El-Rufai ya kuma yaba wa daliban bisa jajircewa da nuna kwazon tserewa daga hannun ‘yan ta’addan.

Sojoji sun harbe dan sanda a Borno

A wani labarin, kun ji yadda wasu sojoji suka hallaka wani dan sandan da ke bakin aiki a wani yankin jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin Najeriya.

Wannan ya faru ne a lokacin da dan sandan ya kama wani soja dauke da tabar wiwi a cikin wata motar da yake ciki.

Ya zuwa yanzu, ana ci gaba da bincike don gano tushen lamarin kafin daga bisani a dauki matakin da ya dace.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.