Rundunar Yan Sanda Ta Sallami Jami’anta Da Ke Ba Wa Rarara Tsaro

Rundunar Yan Sanda Ta Sallami Jami’anta Da Ke Ba Wa Rarara Tsaro

  • An kori jami'an yan sandan da ke tsaron shahararren mawakin APC, Dauda Adamu Kahutu wanda aka fi sani da Rarara
  • Jami'in hulda da jama'a na rundunar Olumuyiwa Adejobi ne ya sanar da batun korar jami'an a ranar Alhamis, 13 ga watan Afrilu
  • Adejobi ya ce an sallami jami'an uku da aka hada da mawakin don ba shi kariya ne daboda barnatar da harsasai

Rundunar yan sandan Najeriya ta sallami jami’anta da ke ba shahararren mawakin siyasa, Daura Adamu Kahutu Rarara tsaro, a ranar Alhamis, 13 ga watan Afrilu, Daily Trust ta rahoto.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, wanda ya sanar da hukuncin a hedkwatar rundunar da ke Abuja, ya ce an kori jami’an ne saboda barnatar da harsasai.

Mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara da jami'an da aka kora
Rundunar Yan Sanda Ta Sallami Jami’anta Da Ke Ba Wa Rarara Tsaro Hoto: Rarara, Police
Asali: UGC

A kwanaki ne aka hasko masu tsaron mawakin a wani bidiyo suna harba harsashi a sama yayin da Rarara ke hanyarsa ta shiga motarsa a Kano.

Kara karanta wannan

Yan Fashi Da Makami Sun Kai Mummunan Hari Kasuwar Ogun Da Tsakar Rana, Sun Kashe Wani Dan Kasuwa

Wannan abu da suka aikata ya haddasa cece-kuke sannan rundunar yan sandan ta sha alwashin daukar mataki.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Wani bangare na sanarwar na cewa:

Bayan korafe-korafe da bincike kan bidiyo da ya yadu a ranar Juma’a 7 ga Afrilu, 2023, a kafafen soshiyal midiya na izza, rashin sanin makamar aiki, da kuma amfani da makamai ba bisa ka’ida ba da wasu yan sanda daga sashin ba da kariya na musamman (SPU) sashi na 1, Kano suka yi, an kori jami’ai uku daga sashin SPU 1 Kano kan laifin amfani da makamai ba bisa ka’ida ba, cin mutuncin aiki, rashin da’a, da kuma barnatar da harsasai.
“An hada jami’an uku, Sufeto Dahiru Shuaibu, Sajan Abdullahi Badamasi da Sajan Isah Danladi da mawakin don aikin ba shi kariya. Da suke bakin aiki a ranar 7 ga watan Afrilun 2023 a kauyen Kahutu, jihar Katsina, jami’an sun yi harbe-harbe a sama daga makaman aikinsu duk da tsarin aikin yan sanda bai yarda da harbi a iska ba, da kuma yin watsi da hatsarin da hakan zai iya haifarwa ga taron jama’ar da ke wajen harda yara. Wannan ba iya laifi da rashin sanin makamar aiki bane kawai harda tozarta rundunar da kasar baki daya."

Kara karanta wannan

Allahu Akbar: Wani Babban Jami'in Kotun Musulunci Ya Rasu Ta Hanya Mai Ban Tausayi a Watan Azumi

Daga karshe rundunar yan sandan ta gargadi jami'anta da su tabbata sun aiwatar da ayyukansu daidai da tsarin doka a duk lokacin da suke bakin aiki.

A wani labari na daban, mun ji cewa jami'an tsaron kasar Ingila sun tsare tare da yi wa dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party, Peter Obi tambayoyi a filin jirgin sama a Landan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng