Sarkin Kano Aminu Ado Bayero Ya Yi Sauye-Sauye a Majalisarsa, Ya Yi Sabbin Nade-Nade

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero Ya Yi Sauye-Sauye a Majalisarsa, Ya Yi Sabbin Nade-Nade

  • Masarautar Kano ta yi sabbin nade-nade tare da sauyawa wasu mukamai a wannan karon, ta fadi dalilin yin hakan a yanzu
  • Wannan na zuwa ne bayan kammala zaben gwamnoni a Najeriya, inda jihar ta samu sabon gwamna dan jam’iyyar NNPP
  • A bangare guda, kun ji yadda ‘yan siyasar Kano suka fara musayar yawu tun bayan sanar da sakamakon zaben gwamnan jihar

Jihar Kano - Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero ya yi garanbawul ga majalisarsa, inda ya daga darajar wasu daga cikin manyan na kusa dashi da suka nuna kwazo wajen yin aikinsu.

Hakazalika, ya yi sabbin nade-nade a masarautar domin yiwa al'ummar Kano aiki yadda ya dace kamar yadda aka saba.

Wannan batu na fitowa ne daga wata sanarwar da sakataren masarautar, Abubakar Balarabe Kofar Naisa ya fitar, Leadership ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Zaben Kogi: Jerin jiga-jigan siyasan APC 3 da ke son maye gurbin Yahaya Bello da tasirinsu

Masarautar Kano ta yi sabbin nade-nade
Masarautar Kano, a Arewacin Najeriya | Hoto: dailytrust.com
Source: UGC

Wadanda aka sauyawa mukamai

Daga cikin wadanda aka kara wa matsayi a masarautar akwai Alhaji Ahmad Ado Bayero daga sarkin gida zuwa Dan Iyan Kano, sai kuma Turkakin Kano, Alhaji Lamido Sanusi Bayero zuwa mukamin sarkin gida.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Hakazalika, an ba Tafidan Kano, Alhaji Mahmud Ado Bayero mukamin Turakin Kano sai kuma Dan Galadiman Kano, Alhaji Haruna Rasheed Sanusi da ya zama Tafidan Kano.

Har ila yau, Alhaji Kabiru Tijjani Hashim, Dan Isan Kano ne ya zama sabon Dan Galadima a masarautar mai dimbin tarihi, Punch ta ruwaito.

Sauran sun hada da Dan Lawan Kano, Alhaji Bashir Ado Bayero da ya zama sabon Lawan Kano da kuma Alhaji Yahaya Inuwa Abbas Dan Majen Kano da ya zama Dan Lawan Kano.

Sabbin mukamai

A bangaren sabbin nade-nade, an yiwa Alhaji Ahmad Kabiru Bayero matsayin sabon Barde Kerarriya da kuma Alhaji Abdulkadir Mahmud a matsayin sabon Magajin Rafin Kano.

Kara karanta wannan

IWD: Hadiza Sabuwa da Matan da Aka Rantsar a Kujerar Mataimakan Gwamnoni

Da yake magana bayan wadannan nada-naden, sarkin Kano Bayero ya ce, an ba da mukaman ne bisa la’akari da kwazo da bajintar da suka nuna.

Ya kuma bukace su da su kasance masu wakiltar masarautar Kano da suna mai kyau a duk inda suka tsinci kansu kuma su yi aikinsu don ci gaban masarauta.

A baya, kunji yadda Abba Kabir Yusuf, sabon gwamnan Kano ya shawarci duk wadanda ke gini a filayen gwamnati da su gaggauta dakatar da ginin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng