IPOB Ta Shiga Jerin Kungiyoyin Yan Ta'adda 10 Mafi Hatsari a Duniya

IPOB Ta Shiga Jerin Kungiyoyin Yan Ta'adda 10 Mafi Hatsari a Duniya

Rahoton ta'addanci na duniya (GTI) ya sanya IPOB a cikin jerin ƙungiyoyin yan ta'addda 20 masu haɗari a duniya.

Ƙungiyar masu fafutukar kafa ƙasar Biafara (IPOB) ta kai matsayi na 10 a cikin jerin ƙungiyoyin 'yan ta'adda mafi haɗari a faɗin duniya.

Shugaban IPOB, Nnamdi Kanu.
DSS sun raka shugaban IPOB zuwa wajen Kotun tarayya Hoto: Kola Sulaiman/AFP
Source: UGC

Makarantar tattalin arziki da kuma bin diddigin ayyukan ta'addanci a duniya ce take wallafa rahoton GTI. A sabon rahoton da ta fitar ranar Talata 14 ga watan Maris, IPOB na matsayi na 10.

Jerin ƙungiyoyin 'yan ta'adda 20 mafi hatsari a duniya

Matsayi

Sunan kungiya

Adadin kisa

Hare-hare

Yawan masu rauni

1

IS

1045

410

644

2

Al-shabaab

784

315

1016

3

IS ta lardin Khorasan

498

141

132

4

Jama'atu Nusrat Islam (JNIM)

279

77

215

5

Balochistan Liberation Army (BLA)

233

30

113

6

Islamic State West Africa (ISWAP)

219

65

118

7

Boko Haram

204

64

51

8

Taliban ta Pakistan

137

90

187

10

Yan awaren IPOB

57

40

16

11

Kurdistan Workers Party (PƘK)

40

54

150

12

Communist Party a Indiya

39

61

30

13

Al-Qaeda ta yankin larabawa (AQAP)

17

6

23

14

FARC ta ƙasar Colombia

16

17

37

15

New Peoples Army (NPA)

19

13

25

16

Ƙungiyar LeT

8

6

38

17

Balochistan Liberation Front (BLF)

6

4

8

18

National Liberation Army (ELN)

5

28

77

19

Islamic Jihad

5

2

10

20

Belochistan Republic Army

4

1

8

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Ana Dab Da Zabe, 'Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Sakataren APC a Jihar Rivers

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

IPOB ta kafa tarihin a shekarar 2022 - GTI

A cewar rahoton aikata ta'addanci na duniya (GTI), ƙungiyar IPOB ta kaddamar da hare-hare da kashe-kashe mafi yawa a tarihinta a shekarar 2022.

"Kungiyar IPOB, wacce gwamnatin Najeriya ta ayyana a matsayin ƙungiyar ta'addanci ta aikata ta'asa mafi muni a 2022. Su ke da alhakin kai hare-hare 40 da kisan 57 a 2022."

"Hakan ya nuna an samu karin hare-hare 26 da kisan mutane 34 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabaci 2022," inji rahoton.

A wani labarin kuma Najeriya ta koma matsayi na 36 a jerin kasashe masu karfin sojoji 145 na faɗin duniya

A sabon rahoton da aka fitar, Najeriya ta samu koma baya da matsayi ɗaya, daga matsayi na 35 zuwa matsayi na 36 a duniya.

Haka zalika a jerin kasahen nahiyar Afirka, Najeriya ta sake matsawa baya da matsayi ɗaya a sabon rahoton.

Kara karanta wannan

Jerin Mata 24 Da Ke Takarar Kujerar Gwamna a Zaben Ranar Asabar

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262