Ina Bukatar N70m ‘Nakadan’ Domin Hidimin Zabe, Inji Dan Majalisa Ado Doguwa
- Yayin da zabe ya matso, dan majalisar wakilai a Najeriya ya bayyana bukatar a samu kudi don gudanar da aikin zabe
- Ado Doguwa ya koka da cewa, doka ta bashi damar rike N70m kafin zabe, amma bai samu ba
- ‘Yan Najeriya; ‘yan siyasa da gama-gari na ci gaba da kuka kan yadda batun kudi ke kara ta’azzara
FCT, Abuja - Dan majalisar wakilai a matakin tarayya, Ado Doguwa ya bayyana cewa, rashin kudi tsaba a hannu zai shafi zaben 2023 mai zuwa, musamman ga ‘yan siyasa.
A cewarsa, akalla yana bukatar tsabar kudi a hannu da suka kai N70m a lokacin zaben da ke tafe nan ba da jimawa ba, Channels Tv ruwaito.
Ya bayyana wannan batun ne bayan ganawa da shuganan kasa Muhammadu Buhari a fadarsa da ke Aso Rock a Abuja a ranar Alhamis kan batun ka’idojin kudi.

Kara karanta wannan
Alkawari kaya ne: Tinubu ya fadi abu 1 da zai yiwa ASUU kowa ma ya huta idan ya gaji Buhari

Asali: Getty Images
Doguwa ya shaida cewa, sashe na 88(9) na kudin zabe ya bashi damar samun akalla N70m domin kudanar da harkar zabe, amma bai samu ba.
DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka
Kudi nake bukata masu yawa
A cewarsa:
“Ina bukatar tsabar kudi N70m. Wannan shine matsayar doka amma da nake magana daku yanzu bani dasu.”
Ya kara da cewa, wannan ka’idar takaita kudi a hannun jama’a zai shafi ‘yan siyasar da ke neman kujerun takara ba tare da la’akari da jam’iyyarsu ba.
A cewarsa, a wurare da yawa, babu bankuna ko injin ATM don tabbatar da agent-agent da sauran ma’aikatan na zabe sun samu hakkinsu a lokacin zabe, TheCable ta ruwaito.
Dokar nan ta shafi kowa
Ya kuma koka da cewa, wannan dokar ta shafi jam’iyya mai mulki da ma jam’iyyun adawa da ke ‘yan takara a zaben bana.
Da yake martani ga dokar kudi ta CBN:
“Wasu daga cikinmu suna ganin abin alheri game da ka’idar, amma damuwar a matsayinmu na ‘yan majalisa na jam’iyya mai ci shine, meye yasa sai yanzu?”
Doguwa ya jaddada cewa, bai kamata a kawo batun sauyin kudi da sanya ka’idojin kayyade kudi a hannun jama’a ba kwanaki kasa da 40 kafin zabe.
A tun farko, hukumar zabe ta bayyana yadda karancin kudi zai iya shafar zaben 2023 da ke tafe nan ba da jimawa ba.
Asali: Legit.ng