Tashin Hankali Yayin da Aka Kone Bankuna Biyu a Jihar Delta, ’Yan Sanda Sun Magantu

Tashin Hankali Yayin da Aka Kone Bankuna Biyu a Jihar Delta, ’Yan Sanda Sun Magantu

  • Yayin da 'yan Najeriya ke fuskantar karancin sabbin Naira, wasu na daukar zafi da kuma yin barna a wasu jihohin
  • An kone wasu bankuna biyu a jihar Delta yayin da zaga-zanga ta barke a wata karamar hukumar jihar
  • Ya zuwa yanzu an kama mutane tara da ake zargin suna da hannu a wannan aika-aika, ana ci gaba da bincike

Jihar Delta - Rundunar ‘yan sandan jihar Delta ta bayyana cewa, akalla bankuna biyu aka kone saboda barkewar rikici yayin zanga-zangar karancin kudi a jihar.

Daily Trust ta ruwaito yadda wasu masu zanga-zanga suka mamaye tituna saboda gaza samun sabbin kudade a bankunan jihar.

Da yake martani ga faruwar lamarin, mai magana da rundunar ‘yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe ya bayyana yadda lamarin ya zo da tsaiko.

Kara karanta wannan

Karin Bayani: Fusatattun Mutane Sun Bankawa Bankuna da ATM Wuta Kan Karancin Naira

An kone bankuna a Kudu
Tashin Hankali Yayin da Aka Kone Bankuna Biyu a Jihar Delta, ’Yan Sanda Sun Magantu | Hoto: David Darius
Asali: Getty Images

A cewarsa, an kama mutane tara da zargin suna hannu da kone wasu bankuna biyu na kasuwanci a karamar hukumar Udu ta jihar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An kama mutane tara, ana ci gaba da bincike

Ya bayyana hakan ne a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana rashin amincewar rundunar ‘yan sanda da ayyukan ta’addanci babu gaira babu dalili.

A kalamansa:

“A karamar hukumar Udu, wasu tsagerun matasa da sunan zaga-zanga sun kone bankuna biyu da ababen hawa a karamar hukumar Udu.
“Mun kama tara da muke zargi zuwa yanzu. A hakan wasu za su kira wannan abu zanga-zanga.”

'Yan Najeriya na ci gaba da zanga-zanga a yankuna daban-daban na kasar nan kan lamarin da ya shafi karancin kudi da kuma cunkoso a bankunan kasuwanci.

Tuni dai aka daina amfani da tsoffin N200, N500 da N1000 a kasar, inda aka kirkiri sabbi amma samunsu ya gagara a hannun atalakawan kasa.

Kara karanta wannan

Alkawari kaya ne: Tinubu ya fadi abu 1 da zai yiwa ASUU kowa ma ya huta idan ya gaji Buhari

Akwai kudi a CBN, bankuna sun ki zuwa dauka

A wani labarin kuma, babban bankin Najeriya (CBN) ya daura alhakin karancin sabbin Naira a hannun jama'a ga bankunan kasuwanci na kasar.

CBN ya ce, ya buga sabbin kudade wadatattu, kuma yana jiran bankuna su zo su dauka domin rabawa jama'a a kan kanta da ATM.

A jawabinsa, CBN ya ce bankunan kasuwanci sun ki zuwa domin karbar kudaden, lamarin da ya jawo tsaiko a kasar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel