Dalilin da Ya Sa Gwamnatin Burtaniya Ta Gayyaci Atiku, Majalisar Kamfen Dinsa Ta Magantu

Dalilin da Ya Sa Gwamnatin Burtaniya Ta Gayyaci Atiku, Majalisar Kamfen Dinsa Ta Magantu

  • Atiku Abubakar ya samu gayyata daga gwamnatin Burtaniya, an tattauna dashi kan wasu batutuwa
  • Jam'iyyar PDP ta fito ta yi bayani, ta bayyana gaskiyar abin da dan takarar na PDP ya tattauna da Burtaniya
  • Hakazalika, PDP ta ce akwai haske ga Atiku a zaben shugaban kasa da za a yi nan da wata guda a Najeriya

Najeriya - Majalisar kamfen din takarar shugaban kasa ta jam'iyyar PDP ta bayyana dalilin da yasa gwamnatin kasar Burtaniya ta gayyaci Atiku don tattaunawa dashi, New Telegraph ta ruwaito.

A cewar majalisar, an gayyaci Atiku ne domin tattauna batutuwan da suka shafi gamayya da hadin gwiwa tsakanin Najeriya da Burtaniya a nan gaba idan ya gaji Buhari.

Wannan na fitowa ne daga daraktan yada labaran majalisar, Otunba Dele Momodu a cikin wani sako da ya bayar a jiya Talata 10 ga watan Janairu.

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP: Bana goyon bayan Atiku, ba kuma zan tursasawa 'yan jiha ta su bi ra'ayi na ba

Dalilin da yasa Burtaniya ta gayyaci Atiku don tattaunawa dashi
Dalilin da Ya Sa Gwamnatin Burtaniya Ta Gayyaci Atiku, Majalisar Kamfen Dinsa Ta Magantu | Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Akwai yiwuwar Atiku ya lashe zabe, inji Dele Momodu

Momodu ya kuma bayyana cewa, akwai haske mai kyau game da nasarar Atiku a zaben da za a gudanar a cikin watan Fabrairu mai zuwa, rahoton Vanguard.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A cewar sakon nasa:

"Majiya ciki ta naqalto cewa, zaben ciki gida a na gwamnatin Burtaniya ya nuna AA (Atiku Abubakar) ne dan takarar da kan gaba kuma akwai yiwuwar aiki kafada-kafada dashi don amfanin kasashen biyu.
"Wannan na da matukar muhimmanci domin Burtaniya na son habakawa da fadada alakar kasuwanci da Najeriya."

Rikicin da ke gaban Atiku a matakin jam'iyya

Duk da wannan, har yanzu dan takarar na shugaban kasa a PDP na ci gaba da fuskantar barazana da koma baya a jam'iyyar, kasancewar akwai wasu jiga-jigan jam'iyyar da ke adawa dashi.

Kara karanta wannan

Tinubu Ko Atiku: An Tona Sunan Dan Takarar da Kwankwaso da Peter Obi Suke Wa Aiki a Zaben 2023

Gamayyar gwamnonin G-5 na ci gaba da nuna adawa da shugabancin PDP a matakin kasa, kana sun ce babu ruwansu da Atiku.

Gwamnonin dai burinsu shine; su ga an tsige Ayu Iyorchia ammatsayin shugaban jam'iyyar na kasa tare da ba wani dan yankin Kudu.

Burtaniya ba za ta tsoma baki a zaben bana ba

A tun farko kun ji cewa, kasar Burtaniya ta ce ba za ta sanya baki a zaben da za a gudanar a Najeriya ba kwata-kwata.

Wannan na fitowa ne daga bakin Ms Catriona Laing, babbar kwamishiniyar Burtaniya a Najeriya lokacin da take magana game da zaben na bana.

Ta kuma bayyana cewa, kasar ta Turai za ta tsaya ne tsaka-tsaki kan dukkan abubuwan da za su faru a zaben.

Asali: Legit.ng

Online view pixel