Shehu Sani: An Sace Wayar Namadi Sambo A Wurin Kaddamar Da Littafi A Abuja

Shehu Sani: An Sace Wayar Namadi Sambo A Wurin Kaddamar Da Littafi A Abuja

  • An sace wayar salular tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya Arc Namadi Sambo a babban birnin tarayya Abuja
  • Tsohon sanata mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya ce lamarin ya faru ne wurin kaddamar da littafi kan marigayi Gwamna Solomon Lar
  • Sani ya ce akwai jami'an tsaro matuka a wurin taron amma abin mamaki duk da hakan aka samu wani ya ratsa ya sace wayar tsohon gwamnan na Kaduna

FCT, Abuja - An sace wayar salular tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Arc. Namadi Sambo a wurin wani taro a babban birnin tarayya, Abuja.

Sanata Shehu, tsohon dan majalisar tarayya, wanda ya bayyana hakan a Twitter a ranar Alhamis, ya ce lamarin ya faru ne a wurin kaddamar da littafin "Chronicles Of The Rainbow", tarihin marigayi Gwamna Solomon Lar.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Bola Ahmed Tinubu Ya Diro Najeriya Bayan Kwashe Kwanaki a Turai

Namadi Sambo
Shehu Sani: An Sace Wayar Namadi Sambo A Wurin Kaddamar Da Littafi A Abuja. Hoto: @MobilePunch.
Asali: Depositphotos

Ya ce akwai jami'an tsaro sosai a wurin taron amma wani ya 'kutsa' ya sace wayar salulan.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Ya rubuta:

"Abin mamaki ne yadda wani ya tsallake matakan tsaro ya sace wayar tsohon mataimakin shugaban kasa Sambo a taron kaddamar da litafin marigayi Gwamna Solomon Lar a Abuja."

Sambo ne mataimakin shugaban kasar Najeriya daga ranar 19 ga watan Mayun 2010 zuwa 29 ga watan Mayun 2015.

Ya yi gwamna a jihar Kaduna daga 2007 zuwa 2010.

Na yi farin cikin ganin an girmama mahaifi na - Beni Lar

Yayin da ta ke magana da manema labarai, yar Lar, wacce yar majalisar wakilai na tarayya ne, Hon. Beni Lar ta ce:

"Na yi farin cikin ganin an karrama mahaifi na. Ina farin cikin cewa bayan shekaru da ya yi wa Najeriya hidima, ya mutu ba tare da mallakar gida a Abuja ba, wani karamin gida kawai gare shi a Jos. Ya yi wa mutane hidima da dukkan abin da ya ke da shi kuma na ji dadin yadda kowa a kasar nan."

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun fusata, matar Atiku ta ba 'yar sanda ta rike mata jaka a wurin taro

Atiku Ya Fi Kowane Ɗan Takara Cancanta Ya Zama Shugaban Kasa a 2023, Namadi Sambo

wani rahoton, tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, ya bayyana Atiku Abubakar, mai neman zama shugaban kasa a inuwar PDP, a matsayin wanda ya fi dacewa da Najeriya a 2023.

Premium Times tace Sambo ya faɗi haka ne a Abuja a wurin taron gabatar da Litattafai kan Atiku da kaddamar da tawagar yaƙim neman zaɓen PDP.

A cewarsa, ba ko shakka Atiku ne mutumin da zai iya baje matsalolin Najeriya a faifai kuma yake da kwarewar lalubo hanyar warware su baki ɗaya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel