Zahra Buhari Ta Taya Danuwanta Yusuf Da Matarsa Murnar Cika Shekara Daya Da Aure, Ta Saki Kyawawan Hotunansu

Zahra Buhari Ta Taya Danuwanta Yusuf Da Matarsa Murnar Cika Shekara Daya Da Aure, Ta Saki Kyawawan Hotunansu

  • Kamar wasa dan shugaban kasa Muhammadu Buhari, Yusuf Buhari da matarsa kuma diyar sarkin Bichi, Zahra Nasiru Bayero sun shekara da aure
  • Diyar Shugaban kasa, Zahra Buhari-Indimi ta je shafinta na soshiyal midiya domin taya danuwanta da kyakkyawar matarsa murnar zagayowar wannan rana
  • A ranar 20 ga watan Agustan 2021 ne dai masarautar Bichi da ke jihar Kano ta kulla aure tsakanin Yusuf da Zahra Bayero

Najeriya - Shekara ta zagayo da shugaban kasa Muhammadu Buhari da mai martaba sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Ado Bayero suka zama surukai.

Diyar shugaban kasa, Zahra Buhari-Indimi ta taya dan’uwanta, Yusuf da matarsa Zahra Bayero murnar cika shekara daya da aure.

Yusuf Buhari da Zahra, diyar sarkin Bichi, Nasiru Ado Bayero, sun yi aure a ranar 20 ga watan Agustan 2021, a jihar Kano.

Kara karanta wannan

Kwarya Tabi Kwarya: Bidiyoyi Daga Shagalin Bikin Aminu Tajuddeen Dantata Da Aisha Bello Dambazau

A wata wallafa da tayi a shafinta na Instagram a daren ranar Asabar, 20 ga watan Agusta, Zahra Indimi ta wallafa wani bidiyo dauke da hotunan ma’auratan sannan ta rubuta:

“Soyayyarku kyakkyawace matuka. Masha Allah.”
Zahra da Yusuf
Zahra Buhari Ta Taya Danuwanta Yusuf Da Matarsa Murnar Cika Shekara Daya Da Aure, Ta Saki Kyawawan Hotunansu Hoto: mrs_zmbi
Asali: Instagram

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Ba’a Kyauta Mana Mu Talakawa: Rukayya Dawayya ta Koka Kan Yadda ‘Ya’yan Masu Kudi Ke Auran Junansu A Kasar

A wani labarin kuma, Shahararriyar jarumar Kannywood, Rukayya Umar Dawayya ta yi martani a kan yadda ake yin kwarya tabi kwarya wajen kulla auratayya a kasar nan.

Dawayya ta shawarci ‘ya’yan talakawa da ke da kyau a kan su daina yarda da soyayya tsakaninsu da yaran masu kudi domin magana ta gaskiya ba auransu za su yi ba.

A cewarta koda yaran na son su iyayensu ba za su amince a kawo masu diyar talakawa a matsayin suruka ba, don haka ta shawarce su da su tashi su nemi ilimi don gobensu.

Kara karanta wannan

Rigimar Gidan PDP Ta Cabe da Fitowar Tsohon Bidiyon Shugaban Jam’iyya

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng