Jarumar Kannywood Daso ta shiga tseren neman kujerar sanata a Kano

Jarumar Kannywood Daso ta shiga tseren neman kujerar sanata a Kano

  • Jarumar fim Saratu Gidado ta ayyana aniyarta ta son takarar kujerar sanata a babban zaben 2023 mai zuwa
  • Saratu wacce aka fi sani da Daso ta ce za ta yi takarar ne domin ceto kasar daga mawuyacin halin da take ciki a yanzu haka
  • Sai dai kuma, shahararriyar jarumar ta Kannywood ta ce za ta sanar da jam'iyyar da za ta yi takara a ciki nan gaba kadan

Kano - Shahararriyar jarumar Kannywood, Saratu Gidado wacce aka fi sani da Daso, ta bayyana kudirinta na son takarar kujerar sanata a zaben 2023 mai zuwa.

Daso a wata wallafa da ta yi a shafinta na Instagram dauke da fostarta, ta bayyana cewa za ta nemi kujerar ne a mahaifarta ta jihar Kano, amma bata sanar da a kowani yanki bane za ta yi takarar.

Kara karanta wannan

Saraki ya bayyana ainahin abun da ya haddasa rashin tsaro a Najeriya

Sai dai ta kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba za ta sanar da jam’iyyar da a karkashin inuwarta za ta yi takara, inda ta bukaci mutane da su taya ta da addu’a.

Jarumar Kannywood Daso ta shiga tseren neman kujerar sanata a Kano
Jarumar Kannywood Daso ta shiga tseren neman kujerar sanata a Kano Hoto: saratudaso
Asali: Instagram

Ta rubuta a shafin nata:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“#siyasa Barka da safiya ya yan uwana yan Najeriya sannan ina maku barka da karshen mako.
“Ina burin sanar da abin da kezuciyata da kuma sanar da ku cewa zany i takarar kujerar sanata a jihata ta Kano. Nan ba da dadewa b azan sanar da jam’iyyar.
“Ina barar addu’arku ce kawai.
“Manufar: Don ceto kasar daga mawuyacin halin da take ciki. Nagode.”

Jama'a sun yi martani kan haka:

abbaelmustapha1 ya yi martani:

“Ki dauka da muhimmanci dan Allah. Za ki iya cimma hakan.”

sadiya.umar_ibrahim ta ce:

"Wayyo Allah cikina mama"

borno_gidankanshi ta yi martani:

Kara karanta wannan

2023: Maza sun gaza, cikin wata 6 mata da matasa za mu gyara Najeriya, 'Yar takarar APC

"Allah ya zaabah Miki Mafi Alheri "

dr_tafida y ace:

“ALLAH bada Sa’aa mama .”

last_done_backup ya ce:

“HAJIYA MAMA DASO ALLAH Y IDDA NUFI.
“Allah y taya riko”

Jarumin Kannywood, Ali Rabiu Ali, ya fito takarar ɗan majalisar tarayya a 2023

A gefe guda, mun ji a baya cewa jarumi a masana'antar shirya fina-finan Hausa Kannywood, Ali Rabiu Ali, ya tsaya takarar ɗan majalisar wakilan tarayya mai wakiltar mazaɓar Dala ta jihar Kano.

A wata Fasta da jarumin ya saki a shafinsa na Instagram, Ali wanda aka fi sani da Daddy ya nuna cewa yana fatan ya zama magajin Malam Aminu Kano.

Ali wanda Furudusa ne kuma Darakta a Kannywood a ya wallafa Hotonsa ɗauke da Fom ɗin takara karkashin inuwar jam'iyyar PRP.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng