Da Dumi-Dumi: Majalisar Wakilai ta ƙasa ta yi garambawul a sabon kundin zaɓe 2022
1 - tsawon mintuna
Abuja - Majalisar wakilan tarayya ta amince da garambawul a kundin zaɓe 2022 domin bai wa zaɓaɓɓun shugabanni da ke kan madafun iko damar sauke nauyin su a wurin tarukan jam'iyyu da zaɓen fidda gwani.
The Nation ta rahoto cewa Majalisa ta amince da wannan gyara ne a sashi na 84 bayan yin nazari kan kudiri mai taken, "Kudirin garambawul ga dokar kundin zaɓe No. 13 2022 da abin da ya shafi haka."
![Kakakin majalisar wakilan tarayya, Femi Gbajabiamila. Kakakin majalisar wakilan tarayya, Femi Gbajabiamila.](https://cdn.legit.ng/images/1120/43d126ff8bc25d51.jpeg?v=1)
Asali: UGC
Honorabul Abubakar Hassan Fulata shi ne ya ɗauki nauyin gabatar da kudirin gaban takwarorinsa na majalisa kuma suka amince da shi a yau Laraba.
Wannan mataki na zuwa ne awanni 24 bayan majalisar Dattawa ta ƙasa ta amince da yi wa kundin garambawul irin wannan.
Ƙarin bayani na nan tafe...
Asali: Legit.ng