Jerin gyaran fuska 8 da aka yiwa kundin tsarin mulkin Najeriya yau a majalisa

Jerin gyaran fuska 8 da aka yiwa kundin tsarin mulkin Najeriya yau a majalisa

Majalisar dokokin tarayya wacce ta hada majalisar dattawa da majalisar wakilai sun fara kada kuri'a kan sauye-sauye 68 na cigaba da aka gabatar game da garambawul na kundin tsarin mulkin kasa.

A ranar Talata, yan majalisun biyu sun yanke shawara kan wasu ciki.

Yayinda suka amince da wasu gyara-gyaren, sun yi watsi da wasu.

Legit ta tattaro muku jerin abubuwan da yan majalisan suka yi zabe kai a yau:

1. Majalisa ta amince da kudurin takara ga 'yan takara masu zaman kansu

Majalisar dattijai ta amince da kudirin doka mai lamba 58 da ke neman bai wa ‘yan takara masu zaman kansu damar tsayawa takara.

Kudurin zai shafi ‘yan takarar shugaban kasa, na gwamna, da ‘yan majalisun tarayya, da na majalisun jihohi, da na kananan hukumomi.

Kara karanta wannan

Karin bayani: Majalisa ta amince da kudurin takara ga 'yan takara masu zaman kansu

2. Majalisa ta yi watsi da kudirin baiwa yan Najeriya mazauna kasashen waje damar kada kuri'a a zabe

Majalisar dattawa ta yi waje da bukatar baiwa yan Najeriya mazauna kasashen waje damar mushakara a zabukan dake gudana a nan gida.

3. Majalisa ta yi watsi da kudirin baiwa birnin tarayya Abuja Magajin Gari

Majalisa ta ki amincewa da kudirin samar da sabon kujeran magajin gari ga birnin tarayya Abuja.

Jerin gyaran fuska 8 da aka yiwa kundin tsarin mulkin Najeriya yau a majalisa
Jerin gyaran fuska 8 da aka yiwa kundin tsarin mulkin Najeriya yau a majalisa

4. Wajabta nadin dan asalin Abuja matsayin Ministan Abuja

Majalisa ta yi waje da kudirin wajabtawa Shugaban kasa nada dan asalin birnin tarayya Abuja matsayin Ministan garin.

5. Kudirin wajabta ilmi kyauta

Majalisa ta amince da kudirin wajabtawa yara samun ilimi kyauta. Hakazalika ilmi ya zama hakki na dukkan dan Najeriya.

Kara karanta wannan

2023: Dattawan Arewa Sunyi Taro, Sun Yanke Shawarar Goyon Bayan Igbo Ya Maye Gurbin Buhari

6. Majalisa ta amince da dokar tsare arzikin abinci

7. Majalisar tarayya ta kaɗa kuri'ar kin amincewa da kudirin kirkiro wa mata kujeru na musamman

Majalisun dokokin sun yi watsi da dokar samawa mata kujeru akalla 10 a matsayin kwamishanoni a jiha kuma akalla 10 matsayin Ministoci.

Majalisar dattawan ta kaɗa kuri'ar rashin amincewa da dokar kirkiro wa mata kujeru na musamman majalisun tarayya da jihohi. Kudirin dokar ya samu koma baya yayin da Sanatoci 30 suka amince, kuma mutum 58 suka kaɗa kuri'ar kin amincewa.

8. Yan Majalisar Wakilai Sun Ki Amincewa da Fansho Na Har Abada Ga Shugabannin majalisa

Mambobin majalisar wakilai na tarayya sun ki amincewa da wata yunkuri na yi dokar biyan fansho na har abada ga shugabannin majalisar tarayya.

Kuri'u guda 193 ne aka kada a majalisar wakilan na neman bada fansho na har abada ga shugaban majalisar dattawa da kakakin majalisar wakilai da mataimakansu.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Majalisa ta yi watsi da kudurin kirkiro wa mata Kujeru na musamman, da kudirin VAT

Yan majalisa guda 162 sun ce a'a yayin da guda 3 ba su kada kuri'ar ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel