Hoton Khalifa Sanusi II da ‘Ya ‘yansa Mata 3 Yayin da Suka Kammala Digirgir a Landan

Hoton Khalifa Sanusi II da ‘Ya ‘yansa Mata 3 Yayin da Suka Kammala Digirgir a Landan

  • Muhammadu Sanusi II ya dauki hoto da wasu ‘ya ‘yansa mata uku da suka gama karatun digirgir
  • Hafsah (Siddika) Lamido, Shahida Sanusi da Yusra Sanusi sun samu shaidar digirgir a Landan
  • Adam S. Lamido ya ji dadin ganin cigaban da ‘yanuwansa suka samu ta bangaren ilmin zamani

Nigeria - Adam Sanusi Lamido wanda aka fi sani da Ashraf Sanusi, ya yi farin cikin kammala karatun ‘yanuwansa mata har uku.

Da yake magana a dandalin Twitter, Adam Sanusi Lamido ya nuna hotunan ‘yanuwansa bayan sun kammala karatu a jami’a.

Matashin yana mai alfahari ganin yadda Siddika Sanusi, Shahida Sanusi da Yusrah Sanusi suka samu digirgir a birnin Landan.

Ashraf Sanusi ya ke cewa ‘yanuwan na sa sun yi digirinsu na biyu ne a bangaren shari’a da tsare-tsaren jagorancin al’umma.

Kara karanta wannan

Sanatoci na Barazanar Bada Umarnin Cafke Jami’in Gwamnati Kan Bacewar Miliyoyi

Sannan a ‘yanuwansa da suka kammala digirin akwai wanda ta kware a fannin ilmin nazarin Afrika, ita ce 'yar autarsu ukun.

Adam Sanusi Lamido yana alfahari

"Ina mai alfahari da ‘yan kannai na da suka kammala digirgi a bangarorin:

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Daga hagu: (Siddika) @FulaniSiddika
A tsakiya: Tsare-tsaren jagorantar al’umma (Shahida) @shayhee_LS
Daga dama: Ilmin nazarin Afrika (Yusra) @khadijasanusi_
#NewProfilePic
Khalifa Sanusi II da ‘Ya ‘yansa
Siddika Lamido, Shahida Sanusi da Yusra Sanusi Hoto: @Adam_L_Sanusi
Source: Twitter

Ashraf Sanusi ya yi amfani da wannan hoto inda mahaifinsa yake zaune tare da 'ya 'yansa, a matsayin hotonsa a Twitter.

A Disamban nan ne aka ji ‘ya ‘yan tsohon Sarkin na Kano sun kammala karatunsu a jami’ar SOAS da ke Landan a kasar Ingila.

Martanin jama’a a Twitter

Barkansu, Allah ya sa ya amfani al’umma. A wace jami’a suka yi karatu?

- Ummar Safana

Barka ga ‘yanuwanmu.

- Shehu Na Allah

Barkansu duka. Allah ya sa ya yi amfani.

- Aminu Bala

Ina yi masu fatan alheri.

- Bala Tukur Abdullahi

Sarki Sanusi II, mai rajin ganin mata sun yi karatu.

Kara karanta wannan

Sanatan PDP Ya Ba Buhari Uzuri, Ya Fadi Inda Aka Samu Matsala a Gwamnatin APC

- B. G Mamman

Allah (SWT) ya yi masu albarka.

- MB Mai Shela

Barkansu, kuma barka ga Khalifan Tijjaniya.

- Kabir Usman Misali

Kabilancin Larabawa

A baya mun taba jin labari daya daga cikin ‘ya ‘yan tsohon Sarkin Kano, Shahida Sanusi ta zargi Larabawa da bambanci da wariyar launin fata.

Shahida Sanusi wanda take zaune a Saudi Arabiya tayi karin haske daga baya, ta ce ba za a hada Larabawa gaba dayansu, ayi masu kudin goro ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng