Kasar Iran Ta Gano Matsala a Sharuddan Tsagaita Wuta, Ta Shirya Koya Wa Isra'ila Darasi

Kasar Iran Ta Gano Matsala a Sharuddan Tsagaita Wuta, Ta Shirya Koya Wa Isra'ila Darasi

  • Iran ta dauki zafi kan hare-haren da Isra'ila ta sake kai wa kasar Lebanon bayan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin Gabas ta Tsakiya
  • Wani jami'i a gwamnatin Iran ya yi gargadin cewa kasar za ta dauki matakin soji matukar ba a tsawatarwa Isra'ila ba
  • Majiya ta ce dakatar da fada a kowane bangare, ciki har da yakar kkungiyar gwagwarmayar ta Lebanon, na cikin tsarin tsagaita wuta

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Iran - Gwamnatin kasar Musulunci ta Iran ta yi barazanar cewa za ta iya ficewa daga yarjejeniyar tsagaita wuta matukar Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare kasar Lebanon.

Iran ta ce za ta janye daga yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka idan har Isra'ila ta ci gaba da keta yarjejeniyar ta hanyar kai hare-hare a kasar Lebanon.

Iran da Isra'ila.
Jagoran addinin kasar Iran, Mojtaba Khamenei da Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu Hoto: Anadolu Ajensi
Source: Getty Images

Iran ta yi barazanar kai hari Isra'ila

Kara karanta wannan

Bayan cimma matsaya da Iran, sanarwar Shugaba Trump ya raba kan 'yan majalisar Amurka

Wata majiya ce ta bayyana hakan kasa da awanni 24 bayan tsagaita wuta a yakin Amurka/Isra'ila da Iran, kamar yadda tashar Al-Jazeera ta ruwaito.

"Iran za ta fice daga yarjejeniyar idan keta alkawarin tsagaita wuta da gwamnatin yahudawa ke yi ya ci gaba ta hanyar kai hare-hare a Lebanon," in ji majiyar.

Majiyar ta kara da cewa Tehran na nazarin halin da ake ciki a daidai lokacin da ta bayyana hare-haren da Isra'ila ke kai wa Lebanon a matsayin "ci gaba da keta yarjejeniya."

A cewar majiyar, dakatar da fada a kowane bangare, ciki har da yakar "kungiyar gwagwarmayar Musulunci" ta Lebanon, na cikin tsarin tsagaita wutar da Amurka ta amince da shi.

Yadda Isra'ila ta fara karya alkawari

Sai dai, Isra'ila ta "keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta" tun sanyin safiyar ranar Laraba ta hanyar kaddamar da "munanan hare-hare" a kan Lebanon.

Rundunar sojin Isra'ila ta bayyana cewa ta kai hari a wurare sama da 100 "cikin mintuna 10" a yankuna daban-daban a Beirut, kwarin Beqaa da kudancin Lebanon.

Hukumomin kasar Lebanon sun bayyana cewa akalla mutane 1,530 ne aka kashe yayin da wasu 4,812 suka jikkata sakamakon hare-haren na Isra'ila.

Kara karanta wannan

Shirin tsagaita wuta tsakanin Iran, Amurka ya kawo gagarumin sauyi a duniya

Iran ta fusata da halayyar Isra'ila

Wani babban jami'i a Iran ya shaida wa kafar yada labarai ta CBS News cewa kasar "za ta hukunta Isra'ila a matsayin martani ga laifin da ta aikata a Lebanon da kuma keta ka'idojin tsagaita wuta".

"Tsagaita wutar ya shafi yankin baki daya, kuma kowa ya san Isra'ila da karya alkawari, don haka harsashi ne kawai zai iya dakatar da ita," in ji jami'in.

Haka zalika wata majiyar soja da ba a bayyana sunanta ba ta kara da cewa Iran na shirin mayar da martani kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra'ila ta yi.

Yakin Iran.
Yadda ake harba makamai masu linzami zuwa wurare daban-daban a Gabas ta Tsakiya Hoto: Anadolu Ajensi
Source: Getty Images

Netanyahu ya fara shirin karya yarjejeniya

A baya, kun ji cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya ce tsagaita wutar Amurka da Iran ba ta shafi Lebanon ba duk da an ambaci haka a cikin yarjejeniyar.

Ya ce Isra’ila na goyon bayan matakin da Amurka ta dauka na dakatar da hare-hare kan Iran na wucin gadi, amma ya jaddada cewa tsagaita wutar ba ta shafi Lebanon ba.

Netanyahu ya ce Isra’ila na goyon bayan kokarin Shugaban Amurka Donald Trump na tabbatar da cewa Iran ba ta zama barazanar nukiliya da makamai masu linzami ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262