Tsagaita Wuta: Jerin Sharuda 10 Masu Tsauri da Kasar Iran Ta Gindaya wa Amurka
Iran – Bayan sanarwar Shugaba Donald Trump na tsagaita buɗe wuta, an samu bayani dalla-dalla kan sharuda 10 da ke kunshe a daftarin sulhun da Tehran ta gabatar wa Amurka.
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Wannan daftari, mai dauke da sharudda 10, shi ne wanda Trump ya bayyana a matsayin "ginshiƙi mai kyau" na tattaunawa domin kawo ƙarshen yakin Gabas ta Tsakiya.

Source: Getty Images
Sharuɗan Iran 10 na tsagaita wuta
Iran ta gindaya waɗannan sharuɗan 10 a matsayin sharar fage na daina dukkan wani gumurzu da sojojin Amurka da kawayenta, kamar yadda Aljazeera ta ruwaito.
Sharuɗan da Iran ta gindaya su ne:
- Dole a tsagaita wuta baki ɗaya a ƙasashen Iraq, Lebanon, da Yemen.
- Dole Amurka ta daina kai dukkan wani hari kan ƙasar Iran har abada.
- Dole a dakatar da dukkan sauran tashe-tashen hankula dake faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya baki ɗaya.
- Iran ta amince za a sake buɗe mashigar tekun Hormuz ga dukkan jiragen ruwa.
- Samar da sababbin dokoki da za su tabbatar da ƴancin zirga-zirga da tsaro a mashigar Hormuz.
- Dole Amurka ta biya dukkan kuɗaɗen diyya domin sake gina ababen more rayuwa da aka lalata a Iran.
- Dole a janye takunkuman tattalin arziki da aka sanya wa Iran baki ɗaya.
- Dole a sakar wa Iran dukkan kadarorinta da kuɗaɗenta da Amurka ta toshe.
- Iran ta yi alƙawarin cewa ba za ta sake neman mallakar kowane irin makamin nukiliya ba.
- Tsagaita buɗe wuta zai fara aiki a dukkan fagen yaƙi nan take idan aka amince da waɗannan sharuɗa.
Tambayoyin da ake neman amsar su
Rahoton BBC ya nuna cewa akwai tambayoyi birjik da ke bukatar amsa game da sanarwar tsagaita wuta da Donald Trump ya fitar.
Tambayar farko ita ce, shin Trump zai bugi kirji cewa ya ci nasara a yakin, ko dai akwai sauran jan daga? Saboda wasu majiyoyi na cewa zai iya ci gaba da kai hare-haren sama idan wa'adin makonni biyu ya kare, kuma daga bisani ya ayyana cewa ya yi nasara a yakin.
A Gabas ta Tsakiya, tambaya daya mai muhimmanci da ake yi ita ce, shin ya dangantakar Amurka da kawayenta za ta ci gaba da kasancewa?
Uwa uba, ana so a ji ita Isra'ila a wace matsaya ta dauki wannan sanarwa ta Trump? Shin za ta ci gaba da kai hari Iran ko za ta dakata?
Iran ta harba makamai kan Israila
Sai dai kuma, 'yan mintuna kadan bayan Trump ya fitar da sanarwarsa, rundunar sojojin Isra'ila (IDF) ta sanar da cewa ta gano tahowar wasu makamai daga kasar Iran.
Rundunar IDF ta ce tsarin tsaron kasar na kokarin ganin ya kakkabe makaman da Iran ta harbo masu, yayin da aka kunna kararrawar gargadi don al'umma su nemi wurin buya tun da wuri.

Source: Getty Images
Trump ya sanar da tsagaita wuta
Tun da fari, mun ruwaito cewa,Shugaba Donald Trump ya dakatar da dukkan hare-hare kan Iran na tsawon makonni biyu biyo bayan shiga tsakani da ƙasar Pakistan ta yi.
Yarjejeniyar tsagaita wutar za ta yi aiki ne kawai idan Iran ta buɗe mashigar tekun Hormuz cikin gaggawa kuma ba tare da wata barazana ba
Rahoton ya nuna cewa farashin ɗanyen mai a duniya ya fara sauka sakamakon wannan mataki da Trump ya dauka, inda man Brent ya sauka zuwa kusan $103.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

