Bayan Barazanar Trump, An Jero Manyan Kadarori 5 da Amurka Za Ta iya Hara a Iran

Bayan Barazanar Trump, An Jero Manyan Kadarori 5 da Amurka Za Ta iya Hara a Iran

Iran – An shiga zaman dari-dari a Iran a yau Talata, 7 ga Afrilu, 2026, inda ake jiran a ga ko Donald Trump zai cika alkawarinsa na kai munanan hare-hare kan kasar.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Shugaban Amurka dai ya yi barazanar kai hare-hare kan manyan gadojin dake fadin kasar Iran, tare da dukkan manyan kadarorin kasar, ma damar ba a bude mashigar Hormuz ba.

Trump ya yi barazanar farmakar gadojin Iran
Gadar Sadr da ke Tehran, babban birnin kasar Iran. Hoto: @LivinginTehran
Source: Twitter

Barazanar Donald Trump na farmakar gadojin Iran

Kafar watsa labaran Aljazeera ya gudanar da bincike kan wasu gadoji biyar da Amurka za ta iya farmaka, wadanda kai masu hari zai haifar da gagarumar asara ga Iran.

Wannan barazana na zuwa ne kwanaki kalilan bayan da sojojin Amurka suka riga suka nuna karfinsu ta hanyar kai hari kan gadar B1 dake Karaj, a kasar ta Iran.

Kara karanta wannan

Shugaban Iran da mutum miliyan 14 za su kare wuraren da Trump zai ruguza

Wannan danyen aiki ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula takwas, inda masana suka kwatanta matakin a matsayin babban laifin yaki saboda nufin kai hari kan farar hula.

Gadojin da ke cikin hatsari a Iran

Masu bincike sun ayyana wadannan gadoji biyar a matsayin masu matukar muhimmanci ga Iran:

1. Gadar Lake Urmia

Wannan gadar mai tsawon kilomita 1.7 dake tsakanin jihohin Azerbaijan ta Gabas da ta Yamma, ita ce ke hada manyan biranen Tabriz da Urmia.

Farmakar wannan gadar na iya haifar da mummunar matsalar muhalli ga tafkin Urmia tare da tsayar da zirga-zirgar fararen hula.

2. Gadar The Persian Gulf

Wannan wata babbar gada ce mai tsawon kilomita 3.4 da ake kan gina wa a halin yanzu, wadda ke jihar Hormuzgan, kuma ake sa ran za ta hada tsibirin Qeshmu da babban yankin kasar. Ruguza ginshikan ta da aka kafa na iya rusa shirin Iran na shekaru da dama.

3. Gadar Karun 4 Arch

Shahararriyar gada Karun 4 Arch mai tsawon mita 378 dake jihar Chaharmahal-Bakhtiari ita ce ta hada Shahr-e-Kord da Izeh. Tarwatsa ta na iya haifar da gagarumar asara ga wani dam dake kusa da ita.

Kara karanta wannan

Babu sulhu da Iran, Amurka da Isra'ila sun yi babbar barna a garuruwa 12 na kasar Musulunci

4. Gadar Sadr

Wannan gadar dake birnin Tehran ita ce mafi tsawo a daukacin Gabas ta Tsakiya da tsawon kilomita 11, kuma ita ce kusan ruhin zirga zirga a birnin. Hari kan gadar zai iya hallaka fararen hula da yawa da tsayar da ayyukan agajin gaggawa.

5. Gadar Ghadir

Wannan gadar dake Ahvaz tana tsakiyar yankin masana'antun mai da karfe na Iran. Ruguza wannan gadar zai iya raba birnin gida biyu da kuma kawo cikas ga zirga-zirgar iyalan dake yankin, in ji rahoton NDTV.

Trump ya yi barazanar farmakar gadoji da masana'antun makamashin Iran.
Shugaban Amurka, Donald Trump (hagu) da Ministan wajen Iran, Abbas Araghchi (dama) Hoto: Anna Moneymaker / ATTA KENARE via Getty Images
Source: Getty Images

Tasirin barazanar Trump ga Iran

Masana sun bayyana cewa barazanar Trump na daya daga cikin dabarun "durkasa ci gaban kasa" wanda yake son aiwatar wa kan kasar Iran.

Ta hanyar ruguza gadoji da masana'antun makashi, Amurka na son durkusar da tattalin arzikin Iran gaba daya da kuma raba mazauna yankuna daban-daban da junansu.

Trump na barazanar shafe Iran daga duniya

Tun da fari, mun ruwaito cewa, Donald Trump ya gargaɗi Iran cewa zai shafe gaba daya kasar daga doron kasa a daren yau muddin ba ta buɗe mashigar Hormuz ba.

Kara karanta wannan

Iran ta fadi 'bazata' da za ta yi wa Amurka a yaƙi da Isra'ila bayan mata barazana

Rahotanni sun nuna cewa Amurka ta riga sun fara kai hare-hare kan tsibirin Kharg, wanda shi ne babban wurin fitar da man fetur na kasar Iran.

Wannan shi ne karo na huɗu da Trump yake ɗaga wa'adin kai 'mummunan hari Iran,' inda a yanzu ya ce zai shafe kasar da ƙarfe 8:00 na dare.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com