Abu Ya Gagara: Trump zai Janye Yaki da Iran ba tare da Cika Wani Burinsa ba

Abu Ya Gagara: Trump zai Janye Yaki da Iran ba tare da Cika Wani Burinsa ba

  • Shugaban Amurka, Donald Trump ya fara maganar janyewa daga yaki da Iran ta bayan fage bawan shafe wata guda ana gwabzawa
  • Wani rahoto da aka samu daga fadar White House ya nuna cewa Donald Trump ya ce zai janye daga yakin ko ba a bude mashigar Hormuz ba
  • A daya bangaren kuma, Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa bai san lokacin da yakin zai kare ba a halin yanzu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

America - Alamu sun nuna cewa Amurka za ta iya kawo karshen yakin Iran ba tare da cimma wasu abubuwa da Donald Trump ya nema ba.

Shugaba Trump na shan matsin lamba daga cikin kasarsa kan shiga yaki da Iran, inda miliyoyin mutane suka yi zanga-zanga a Amurka.

Kara karanta wannan

Bayan kwadayin man fetur, an gano abin da zai kai sojojin Amurka cikin Iran

Shugaban Amurka, Donald Trump
Shugaba Donald Trump a wajen wani taro. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Yayin da Trump ke son janyewa daga yakin Iran, Times of Israel ta rahoto cewa Benjamin Netanyahu bai nuna alamar kawo karshen rikicin ba.

Donald Trump zai kawo karshen yakin Iran

Shugaban Donald Trump ya ce yana iya kawo ƙarshen yaƙin da ake yi da Iran ko da kuwa mashigar ruwa ta Hormuz ta ci gaba da kasancewa a rufe, inda zai bar batun zuwa wani lokaci na gaba.

Trump da masu ba shi shawara sun yanke hukuncin cewa yunƙurin buɗe mashigar ruwan zai iya tsawaita yaƙin fiye da lokacin da suka tsara na makonni huɗu zuwa shida, kamar yadda jaridar Wall Street Journal ta ruwaito.

An kuma bayyana cewa Trump ya fi mayar da hankali kan lalata makaman roka da rundunar ruwa ta Iran, kafin daga bisani ya matsa mata ta hanyar diflomasiyya domin ta sake buɗe mashigar ruwan.

Dalilan Iran na rufe mashigar Hormuz

Kara karanta wannan

Trump na shirin kara dagula duniya, ya fadi kasar da zai afkawa da yaki

Tehran ta rufe mafi yawan mashigar Hormuz a matsayin martani ga hare-haren haɗin gwiwa na Amurka da Isra’ila, lamarin da ya janyo hauhawar farashin makamashi a duniya.

A Amurka, farashin man fetur ya haura Dala 4 a kan kowane galan a karo na farko cikin fiye da shekaru uku, yayin da yaƙin ke ci gaba da tsananta.

Trump ya ce ana samun “babban ci gaba” a tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin, amma ya yi gargadin cewa idan ba a cimma yarjejeniya ba kuma mashigar ruwan ba ta buɗe nan take ba.

Wani jirgin ruwa a hanyar Hormuz
Yadda jirgin ruwa ke tafiya a hanyar mashigar Hormuz. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

A wani gargadi da ya yi, Trump ya sanar da cewa Amurka za ta kai hare-hare kan cibiyoyin lantarki, rijiyoyin mai da kuma tsibirin Kharg.

Maganar Netanyahu kan yakin Iran

A gefe guda kuma, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce yaƙin da ake yi da Iran ya kusa cimma manufofinsa, amma bai bayyana lokacin da zai ƙare ba.

Ya ce nasarorin sun haɗa da kashe dubban mambobin rundunar Iran, yana mai cewa an kai matakin da ya wuce rabin abin da ake son cimmawa a yakin.

Kara karanta wannan

Bayan Amurka, Trump zai tafi Venezuela neman takarar shugaban kasa

Ana so Najeriya ta rabu da Isra'ila

A wani labarin, mun kawo muku cewa wata kungiyar Musulunci a Najeriya ta nemi gwamnatin Bola Tinubu ta yanke alaka da Isra'ila.

Kungiyar ta ce akwai bukatar Najeriya ta fito ƙarara ta soki kasashen Isra'ila da Amurka kan hare-haren da suka kaddamar a kan Iran.

Bugu da kari, shugaban kungiyar ya yi kira ga kasashen Musulmi su hada kai tare da fatattakar sojojin kasashen waje a yankunan su.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng