Isra’ila Ta Fara Kai Turkiyya Wuya, Ta Gargadi Kasar kan Yakinta da Iran

Isra’ila Ta Fara Kai Turkiyya Wuya, Ta Gargadi Kasar kan Yakinta da Iran

  • Shugaban kasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan ya yi gargadi ga Isra'ila yayin da ake ci gaba da yaki tsakaninta da Iran a yankin Gabas ta Tsakiya
  • Erdogan ya bayyana damuwa ganin yadda yakin Iran da Isra'ila ya jefa Gabas ta Tsakiya cikin mummunan rikici
  • Ya zargi Benjamin Netanyahu da fadada rikici zuwa kasashe kamar Lebanon da sauransu wanda ya jawo asarar rayuka da dukiyoyi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ankara, Turkey - Shugaban kasar Türkiya, Recep Tayyip Erdogan, ya ja kunnen Isra'ila kan ci gaba da yaki da ake yi a Gabas ta Tsakiya.

Erdogan ya gargadi cewa yakin da aka fara kan Iran na kara jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin rikici mai tsanani.

Turkiyya ta fusata game da yakin Iran da Isra'ila
Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian da Shugaban Turkiyya, Racep Tayyib Erdogan. Hoto: @trpresidency/Masoud Pezeshkian.
Source: Twitter

Erdogan ya caccaki Netanyahu kan yakin Iran

Erdogan ya yi wannan bayani ne yayin wani taron jam’iyyarsa a Ankara inda ya ce yakin ya jefa yankin cikin mawuyacin hali mafi muni cikin shekaru 100, cewar TRT World.

Kara karanta wannan

Magana ta fito: Trump ya fadi masu kawo masa cikas a nasarar yaki da Iran

Ya ce:

“Yakin da aka fara da Iran na kara nutsar da yankinmu cikin jini da tashin hankali, inda yara da ba su da laifi ke fuskantar hare-haren makamai.”

Shugaban ya kuma zargi Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, da fadada rikicin fiye da Iran zuwa wasu kasashe.

Ya bayyana cewa gwamnatin Netanyahu na kokarin aiwatar da shirin mamaye Lebanon a hankali, duk da karya dokokin kasa da kasa.

Erdogan ya jaddada cewa Türkiya ba za ta yi shiru ba kan wahalar da al’ummar yankin ke sha, yana mai cewa ba sa bambancewa tsakanin makwabta.

Ya ce:

“Ba za mu taba watsi da abokanmu da ‘yan uwarmu a lokacin wahala ba, kuma ba za mu yi shiru ba kan radadin da suke ciki.”
Erdogan ya gargadi Isra'ila kan yaki da Iran
Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan yayin taro a Ankara. Hoto: Anadolu.
Source: Getty Images

Erdogan ya bayyana illar yakin Iran da Isra'ila

Shugaban ya kuma nuna damuwa kan yadda rikicin ke haddasa asarar rayuka, yana tambaya ko akwai bambanci tsakanin hawaye da ake zubarwa a biranen Iran da na sauran yankuna.

Kara karanta wannan

Ana tsakiyar musayar wuta, Iran ta samu gagarumin goyon baya a yaki da Amurka

Ya kara da cewa duk da cewa rikicin na Isra’ila ne, amma sakamakonsa na shafar Musulmi da kuma bil’adama gaba daya, cewar Daily Sabah.

Erdogan ya kuma gargadi kan dabarun raba kawuna, yana mai cewa dole ne al’ummomin yankin su zauna tare bayan rikicin ya lafa.

Ya kuma soki hana gudanar da ibadar Sallah a Masallacin Kudus, yana mai cewa hakan cin zarafi ne ga Musulmi biliyan biyu.

A karshe, ya jaddada cewa Türkiya za ta ci gaba da bin manufofin diflomasiyya na zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba ga kowa.

Erdogan ya tattauna da shugaban Iran

A baya, kun ji cewa shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan ya yi waya da Shugaban Masoud Pezeshkian na Iran domin tattauna rikicin yankin.

Tayyib Recep Erdoğan ya jaddada cewa Türkiye na son buɗe ƙofa ga diflomasiyya domin rage tashin hankali a Gabas ta tsakiya.

Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian ya ce makaman roka da suka shiga sararin samaniyar Türkiye ba daga Iran suka fito ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.