Trump Ya Yi Magana da Babban Jigo a Tsaron Amurka Ya Yi Murabus saboda Yaki da Iran

Trump Ya Yi Magana da Babban Jigo a Tsaron Amurka Ya Yi Murabus saboda Yaki da Iran

  • Shugaban Amurka Donald Trump ya mayar da martani kan murabus din babban jami’in yaki da ta’addanci Joe Kent
  • Kent ya yi murabus ne daga mukaminsa ne saboda adawa da harin da Amurka da Isra'ila ke yi kan Iran
  • Trump ya bayyana cewa tun farko yana ganin Kent mai rauni ne wajen tsaro, yana mai cewa bai san shi sosai ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Washington DC, US - Shugaban Amurka Donald Trump ya yi martani kan murabus din babban jami’in yaki da ta’addanci, Joe Kent

Majiyoyi sun tabbatar da cewa Kent ya yi murabus ne saboda nuna adawa da matakin Amurka na kai hari kan Iran.

Trump ya soki jami'in tsaron Amurka da ya yi murabus
Joseph Kent, daraktan cibiyar yaki da ta'addanci a Amurka da ya yi murabus tare da Shugaba Donald Trump. Hoto: @joekent16jan19.
Source: Twitter

Legit Hausa ta samu martanin Trump ne a wani faifan bidiyo da Fox News ta wallafa a yammacin yau Talata 17 ga watan Maris, 2026.

Kara karanta wannan

Wani daraktan tsaron Amurka ya yi murabus kan yaki da Iran, ya tona asirin Trump

Musababbin murabus din Joseph Kent

Wannan martani na zuwa ne bayan Kent ya ajiye aikinsa saboda rashin amincewa da tsarin Trump na yakar Iran ba bisa ka'ida ba.

Joseph Kent ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban cibiyar yaƙi da ta’addanci ta Amurka, kan yadda Donald Trump ke yaki da kasar Iran.

Tsohon daraktan ya zargi gwamnatin Trump da fara yaƙi da Iran sakamakon matsin lambar da ta samu daga ƙasar Isra'ila da wasu masu fada a ji.

A cikin wasiƙar da ya aika wa Trump, Kent ya gargaɗi Amurka cewa yaƙin Iran wata makarkashiya ce da aka shirya, kamar yadda aka yi a Iraki.

Trump ya soki murabus din Kent a Amurka
Shugaba Donald Trump na kasar Amurka. Hoto: Al Drago/Bloomberg.
Source: Getty Images

Murabus din Kent: Martanin da Trump ya yi

Trump ya ce tun da farko yana kallon Kent a matsayin mai rauni a fannin tsaro, yana mai cewa bai san shi sosai ba, amma yana ganin mutum ne mai kirki a dabi’a.

Sai dai Trump ya ce bayan ya karanta bayanin da Kent ya fitar, ya fahimci cewa ya fi dacewa ya bar mukamin, saboda ya bayyana cewa Iran ba ta zama barazana ga tsaro ba.

Kara karanta wannan

Trump ya yi magana kan amfani da makamin nukiliya a yaki da Iran

Ya ce:

“Na dade ina tunanin cewa yana da rauni wajen tsaro. Rauni sosai a bangaren tsaro. Ban san shi sosai ba. Amma na ga kamar mutum ne mai kirki.
"Amma lokacin da na karanta bayaninsa, na fahimci cewa alheri ne ma ya fita, domin ya ce Iran ba ta zama wata barazana ba.”

Sai dai wasu na ganin murabus din Kent zai bar wagegen gibi a yaki da ta'addanci da Amurka ke yi saboda kwarewarsa, cewar The Hill.

Yakin Iran: Gargadin da aka yi wa Trump

An ji cewa shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya samu gargadi kan abin da zai iya faruwa idan aka kai wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Majiyoyi sun bayyana cewa an sanar da shugaban na Amurka cewa akwai abubuwan da Iran za ta iya yi muddin aka kai mata hari.

Daga cikin abin da aka sanar da Trump shi ne Iran za ta iya rufe mashigar ruwa ta Hormuz wadda ke da matukar muhimmanci wajen jigilar kayan makamashi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.