Amurka Ta Je Barbara, Za Ta Iya Dawo wa da Ciki a Yakin Iran
- Masanin harkokin tsaro, Joe Cirincione ya ce dogon yaƙi na iya sauya siyasar Amurka fiye da ta daular Musulunci ta Iran
- Ya bayyana haka ne a yayin da yakin da Amurka da Isra'ila suka fara da Iran ya shiga rana ta 13 ana ci gaba da gwabzawa
- Joe Cirincione ya bayar da tabbacin cewa tarihi ya nuna cewa yaƙe-yaƙe kan sauya ra’ayin jama’a da tsarin shugabanci a ƙasashe
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
USA – Masanin harkokin tsaro Joe Cirincione ya bayyana cewa duk wani yaƙi mai tsawo a duniya kan iya haifar da sakamako na siyasa da ba a zata ba.
Joe Cirincione ya bayyana haka ne bayan gwamnatin Amurka da Isra'ila sun sha kiraye-kiraye ga 'yan Iran su karbe gwamnati bayan kashe Ayatollah Ali Khamnei.

Kara karanta wannan
Lauya ya kitsawa gwamnatin Tinubu yadda za ta tursasa wa Trump kawo karshen yaki da Iran

Source: Facebook
A wani nazari da aka wallafa a shafin Facebook na World Times Institute, Joe Cirincione ya kara da cewa yakin zai iya kawo canji a cikin manyan ƙasashe kamar Amurka.
An yi wa Amurka mummunan hasashe
A wata nazarin da ya gabatar, Cirincione ya ce akasari mutane kan ɗauka cewa irin waɗannan rikice-rikice sukan fi girgiza ƙasashen da ake kai wa hari, kamar Iran.
Sai dai a cewarsa, tarihin duniya ya nuna cewa wani lokaci sakamakon siyasar da yaƙi ke haifarwa kan fi bayyana a ƙasashen da ke shiga yaƙin.

Source: Getty Images
Ya ce idan rikici ya daɗe yana gudana, yana iya canza yadda jama’a ke kallon gwamnati da shugabanni, wanda hakan kan iya sa a samu matsin lamba ga masu mulki.
A cewarsa, irin wannan yanayi na iya haifar da sauyi a cikin siyasa, musamman idan jama’a suka fara tambayar dalilin yaƙin ko kuma yadda gwamnati ke tafiyar da al’amura.
Yadda yaki da Iran zai shafi Amurka
Joe Cirincione ya yi nuni da cewa tarihin duniya ya nuna misalai da dama inda rikice-rikicen yaƙi suka haifar da sauye-sauye a cikin tsarin siyasa, ko kuma suka sa shugabanni suka rasa karɓuwa a idon jama’a.
Haka kuma, irin wannan rikici kan sa a samu rarrabuwar ra’ayi a tsakanin al’umma, wanda wani lokaci kan jawo matsin lamba ga gwamnati ta sake duba manufofinta. Cirincione ya bayyana cewa a irin wannan yanayi, shugabanni kan fuskanci ƙalubale wajen tabbatar da cewa suna da goyon bayan jama’a, musamman idan yaƙin ya jawo asarar rayuka ko kuma matsin tattalin arziki.
Ya kara da cewa wannan yaki da Amurka ta tsunduma kanta zai iya jawo canji a cikin kasar fiye da Iran da suke kokarin kawo wa matsala.
Amurka ta tabbatar da bacewar jirginta
A baya, kun ji cewa rundunar sojin Amurka ta tabbatar da bacewar jirgin dakon manta a yammacin Iraki yayin da ake gudanar da farmakin Epic Fury kan kasar Iran.
Jami'an soji sun bayyana cewa ba wai harin makiya ne ya jawo bacewar jirgin ba, kuma ana cigaba da kokarin neman mutanen da ke cikinsa don tabbatar da halin da ake ciki
Wannan ne jirgi na hudu da Amurka ta rasa a yakin Gabas ta Tsakiya bayan an kakkabo jiragen F-15 guda uku a kasar Kuwait bisa kuskure yayin da yakin ya shiga kwana na 13.
Asali: Legit.ng

