Bayan Kashe 'Dan Kasarta, China Ta Maida Martani kan Yakin Iran da Amurka, Isra'ila

Bayan Kashe 'Dan Kasarta, China Ta Maida Martani kan Yakin Iran da Amurka, Isra'ila

  • China ta bukaci kasashen Amurka, Isra'ila da Iran su dakatar da kai wa juna hare-hare, su koma teburin tattaunawa domin a samu sulhu
  • Ma'aikatar Harkokin Wajen China ta tabbatar da mutuwar dan kasarta guda daya a Tehran sakamakon hare-haren Amurka da Isra'ila
  • Martanin China na zuwa ne bayan shiga kwana na uku a yakin da ya barke tsakanin Amurka, Isra'ila da Iran, wanda ya yi sanadin rasa rayuka

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

China - Kasar China ta nuna damuwa kan rikicin da ke kara zafi a Gabas ta Tsakiya bayan barkewar yaki tsakanin Amurka, Isra'ila da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

A safiyar yau Litinin, China ta yi kira da a tsagaita wuta, a koma kan teburin tattaunawa domin kawo karshen rikicin Gabas ta Tsakiya, yayin da yake shiga rana ta uku.

Kara karanta wannan

Hatsabiban makamai da Iran ta mallaka yayin da take yaki da Amurka da Isra'ila

Xi Jinping da Trump.
Shugaban kasar China, Xi Jinping da takwaransa na Amurka, Donald Trump Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Tashar NBC News ta tattaro cewa Isra'ila da da Amurka na ci gaba da kai hare-hare kan Iran da Lebanon, inda rikicin ya bazu zuwa makwabtan yankin.

China ta kawo mafita a yakin Iran

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen China, Mao Ning, a taron manema labarai, ta bukaci a warware matsalar da jawo yakin tsakanin kasashen uku ta hanyar tattaunawa da sulhu.

Ning ta ce:

“Mafi muhimmanci a yanzu shi ne tsagaita wuta da kuma hana rikicin yaduwa a Gabas ta Tsakiya."

An kashe 'dan kasar China a Tehran

Ta ce wani 'dan kasar China daya ya mutu sakamakon yakin a Tehran, inda Isra’ila da Amurka ke kai hare-hare a wani samame da aka ce ya yi sanadin mutuwar jagoran Jamhuriyar Musulunci.

“Ma’aikatar harkokin wajen ta umarci ofishin jakadancin China da ke Iran da ya bayar da taimako ga wanda lamarin ya shafa da iyalansa,” in ji Mao, ba tare da karin bayani ba.

Kara karanta wannan

Yadda Saudiyya ta kakkabo wasu makamai da Iran ta harba a yaki da Amurka

Ta kara da cewa tun farko ba a sanar da China shirin Amurka na kai hari ba, tana mai cewa Beijing da Moscow sun bukaci Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da ya kira taron gaggawa.

China ta gargadi 'yan kasarta kan zuwa Iran

Gwamnatin China ta yi gargadi, a makon da ya gabata ga ’yan kasarta, da cewa kada su yi tafiya zuwa Iran a halin yanzu saboda yanayin tsaro, kamar yadda Arab News ta kawo.

Sama da ’yan kasar China 3,000 ne aka ruwaito cewa sun bar kasar Iran zuwa ranar Litinin, 2 ga watan Maria, 2026.

Shugaban kasar Iran.
Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian a wurin taron manema labarai Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Ana sa rana shugaban Amurka, Donald Trump, zai ziyarci China daga 31 ga Maris zuwa 2 ga Afrilu, 2026, a tafiyarsa ta farko zuwa kasar ta Asiya a zangon mulkinsa na biyu.

Da aka tambaye ta game da ziyarar, Mao ta ce Beijing da Washington “na ci gaba da tuntubar juna kan ganawar shugabannin kasashen biyu,” ba tare da bayar da cikakken bayani ba.

Iran ta yi ikirarin kai hari ofishin Netanyahu

A wani rahoton, kun ji cewa Iran ta ce makaman masu linzami na Kheibar da ta harba sun sauka a ofishin Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu da kuma hedkwatar sojin Isra'ila.

Kara karanta wannan

Yawan sojojin Amurka da suka mutu bayan harin Iran, wasu da dama sun jikkata

Wannan hari, wanda Iran ta kira "rukuni na 10" na hare-hare, ya afku ne a matsayin martani ga kashe jagoran ƙasar Ayatollah Ali Khamenei.

Iran ta kuma bayyana cewa makamin Kheibar yana da ikon ratsa dukkan na'urorin kariya na sararin samaniya, ciki har da na Iron Dome.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262