Kisan Kiristoci: Amurka Ta Ware Wasu 'Yan Najeriya, Ta Sanya Masu Takunkumi

Kisan Kiristoci: Amurka Ta Ware Wasu 'Yan Najeriya, Ta Sanya Masu Takunkumi

  • Amurka ta fara daukar matakai da nufin kawo karshen kisan kiyashin da take zargin ana yi wa kiristoci a Najeriya da wasu kasashe
  • A wata sanarwa da ma'aikatar wajen Amurka ta fitar, ta hana bada biza ga wadanda ke da hannu a ayyukan tauye 'yancin addini
  • Ta jaddada cewa kamar yadda Shugaba Donald Trump ya fada, Amurka za ta yi duk mai yiwuwa wajen kare rayukan kiristoci a duniya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Amurka - Gwamnatin Amurka ta fara daukar matakai kan wasu 'yan Najeriya, wadanda take zargin suna goyon bayan kisan kiyashin da ake wa kiristoci a kasar.

Idan ba ku manta ba, Amurka ta sanya Najeriya a jerin kasahen da ake tauye hakkin addini saboda zargin kisan kiristoci.

Shugaba Trump na Amurka.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Rukunin mutanen da matakin Amurka ya shafa

Kara karanta wannan

Aski ya zo gaban goshi: Majalisar Amurka ta fara zama da bincike kan 'kisan Kiristoci'

The Nation ta ruwaito cewa gwamnatin Amurka ta sanya takunkumin hana biza ga duk mutanen da suka jagoranta, suka ba da izini ko suke goyon bayan tauye ’yancin addini a Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar a ranar Laraba mai taken “Yaki da Mugayen Hare-haren da ake kaiwa Kiristoci a Najeriya da Duniya."

Wannan mataki na zuwa ne bayan Majaliar Dokokin Amurka ta yi zama kan karuwar hare-hare a Najeriya, wanda ta bayyana da abin damuwa matuka.

Tun a baya dai Amurka ta ce ba za ta zuba ido tana kallo wasu kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayin Islama na kokarin karar da kiristocin Najeriya ba, cewar The Cable.

Gwamnatin Najeriya ta fito a lokuta daban-daban ta musanta zargin yi wa kiristoci kisan kare dangi, inda ta ce Amurka ba ta fahimci hakikanin matsalar tsaron kasar ba.

A wani bangaren matakan da ta shirya dauka domin kare rayuka kiristoci, gwamnatin Amurka ta sanar da nmtakin hana biza ga duk mai alaka da masu take hakkin addini a Najeriya.

Wane mataki gwamnatin Amurka ta dauka?

Kara karanta wannan

'Ana cikin tsoro,' 'Yan majalisar sun yi zazzafar muhawara kan rashin tsaro

A sanarwar da gwamnatin ta fitar yau Laraba, ta ce:

"Sabon tsarin da muka kawo a karkashin Sashe na 212(a)(3)(C) na Dokar Shige da Fice ta Amurka zai bai wa Ma’aikatar Harkokin Waje damar hana bayar da biza ga mutanen da ke da hannu a ayyuka tauye 'yancin addini.
"Za mu hana biza ga mutanen da suke jagoranta, suka amince, suka bada gudunmawa, suka shiga ko suka aikata wani abu na tauye ’yancin addini. Wannan zai iya shafar iyalansu na kusa idan ta kama."
“Kamar yadda Shugaba Trump ya fada, Amurka ba za ta nade hannu ba yayin da irin wadannan abubuwa ke faruwa a Najeriya da wasu kasashe da dama.
"Saboda haka wannan mataki zai shafi Najeriya da kowace gwamnati ko mutum da ke da hannu a ayyukan take ’yancin addini.”
Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

'Dan bindiga ya harbi sojojin Amurka

A baya, kun ji cewa wani dan bindiga ya bude wa sojoji wuta a kusa da fadar shugaba Amurka, White House da ke birnin Washington DC.

Kara karanta wannan

Wasu 'yan Najeriya 2 sun damfari gwamnatin Amurka, sun girbi abin da suka shuka

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya kai ga rufe fadar shugaban kasar Amurka watau White House na wucin gadi a ranar Laraba, 26 ga watan Nuwamba, 2025.

A lokacin da wannan lamari ya faru, Shugaba Trump yana Florida domin shirye-shiryen biki da aka saba yi a duk shekara.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262