Yadda Sabon Tsarin Shige da Ficen Saudiyya zai Shafi Najeriya da Kasashen Afrika

Yadda Sabon Tsarin Shige da Ficen Saudiyya zai Shafi Najeriya da Kasashen Afrika

Kasar Saudiyya ta sauya dokokin mallakar biza domin samun izinin shiga da zama a kasar wanda hakan zai shafi Najeriya da wasu kasashen Afrika.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Yayin da ake shirye shiryen fara aikin Hajjin shekarar 2025, kasar Saudiyya ta yi sauye sauye da suka shafi izinin shiga garin mai tsarki.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnatin Saudiyya ta takaita izinin shiga da zama a kasar ga baki daga kasashen ketare har 14 a fadin duniya.

Saudiyya
Saudiyya ta sanya dokar da za ta shafi Najeriya da kasashen Afrika. Hoto: Bayo Onanuga
Asali: Twitter

A wannan rahoton, mun tattaro muku kasashen Afrika da dokar za ta shafa da kuma karin haske kan yadda dokar za ta shafi matafiya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kasashen Afrika da dokar ta shafa

Times of India ta rahoto cewa daga ranar 1 ga watan Fabrairu, 2025 Saudiyya ta takaita ba da bizar shiga kasar kai tsaye ga masu ziyarar bide ido, kasuwanci da kuma ziyarar dangi.

Kara karanta wannan

Mayakan Boko Haram 129,000 sun tuba, ana ba 800 horo na musamman

A karkashin sabon tsarin, duk wanda ke neman biza zuwa Saudiyya daga Najeriya da wasu ƙasashe 13 za a takaita masa lokacin shiga da zama a kasar.

Matakin zai yi tasiri musamman ga 'yan kasuwa, masu yawon buɗe ido da kuma iyalai da ke da 'yan uwa a Saudiyya, domin dole ne su nemi sabuwar biza a duk lokacin da suke son tafiya.

Kasashen da dokar ta shafa a Afrika sun hada da:

  • Najeriya
  • Algeria
  • Egypt
  • Ethiopia
  • Morocco
  • Sudan
  • Tunisia
Bola Tinubu
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu yayin wani taro a Saudiyya. Hoto: Bayo Onanuga
Asali: Facebook

Dalilan takaita shige da fice a Saudiyya

Hukumomin Saudiyya sun bayyana cewa dalilin canjin shi ne hana amfani da bisa da za ta ba mutum damar shiga kasar a ko da yaushe.

Hukumomin suna ganin hakan zai hana mutum damar aikin Hajji ba tare da izini ba, kuma ana ganin dokar za ta rage matsalar cunkoso a lokutan Hajj.

A shekarar 2024, matsanancin cunkoso da tsananin zafi ya haddasa rasuwar mahajjata sama da 1,200.

Kara karanta wannan

Harsashi ya kare wa dan bindiga yana musayar wuta da sojojin Najeriya

Saboda haka, Saudiyya na fatan wannan mataki zai rage yawan waɗanda ke yin aikin Hajji ba tare da izini ba, tare da tabbatar da tsaro da jin daɗin mahajjata.

Hajji
Cunkoson mahajjata yayin aikin Hajji. Hoto: Inside the Haramain
Asali: Getty Images

Wadanda tsarin Saudiyyan zai fi shafa

Najeriya na daga cikin ƙasashen da sauyin tsarin zai fi shafa, kasancewar ƙasar tana da babbar al’umma da ke yawan ziyartar Saudiyya.

Miliyoyin 'yan Najeriya da sauran kasashen Afrika ne ke tafiya Saudiyya domin kasuwanci, yawon buɗe ido, ibada da ziyartar kabarin Annabi SAW.

Sabon tsarin zai fi tasiri ga:

  • 'Yan kasuwa da ke yawan shiga Saudiyya don harkokin kasuwanci.
  • Iyalai da ke da ‘yan uwa a ƙasar, domin za su riƙa buƙatar sabuwar biza a duk lokacin da za su tafi
  • Masu yawon buɗe ido waɗanda a baya suka fi amfana da damar samun bizar shiga kasar kai tsaye
Kogon Hira
Mahajjata na zuwa Kogon Hira domin bude ido. Hoto: Anadolou
Asali: Getty Images

Yaushe za a janye dokar?

Gwamnatin Saudiyya ta bayyana cewa wannan sauyi na wucin gadi ne, amma ba a bayyana lokacin da za a sake duba lamarin ba.

Kara karanta wannan

"Jihohi za su fara gasa," Gwamnati ta ce kudirin haraji zai farfado da tattalin arziki

Ana sa ran hukumomin Saudiyya za su yi nazari kan tasirin sabon tsarin kafin ɗaukar mataki na gaba.

Saudi
Muhammad bin Salman a wani taro a Saudiyya. Hoto: Inside the Haramain
Asali: Facebook

Me ya kamata matafiya su yi?

Ma’aikatar Harkokin Wajen Saudiyya ta shawarci matafiya da su nemi biza tun kafin lokacin tafiyarsu domin gujewa matsaloli.

An kuma gargadi matafiya da su tabbata sun cika sabbin ka'idojin biza domin gujewa takura a filayen jiragen sama.

Duk da wadannan sababbin ƙa’idoji, Saudiyya na cigaba da kokarin jawo masu yawon buɗe ido daga sassan duniya.

Financial Express ta rahoto cewa kasar na da burin jawo 'yan yawon buɗe ido daga Indiya har miliyan 7.5 a kowace shekara nan da 2030.

Sai dai ana fargabar cewa wannan sabon tsarin zai rage yawan tafiya zuwa Saudiyya a watannin farko na 2025.

Mahajjata
Mahajjatan Kaduna yayin tafiya Saudiyya a lokacin Hajjin 2024. Hoto: Kaduna State Hajj Comission
Asali: Facebook

Jigawa ta yi hadakar noma da Saudiyya

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin jihar Jigawa ta yi hadaka da kamfanin Saudiyya domin habaka noman dabino.

Kara karanta wannan

'Ka taka masa birki': An kai karar El Rufai gaban Nuhu Ribadu, an hango hatsarin kalamansa

Gwamna Umar Namadi ya bayyana cewa yana fatan hadakar ta kai jihar Jigawa matsayin kasa da ta fi samar da dabino a Najeriya da Afrika baki daya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng