'Wani Abu Ya Samu Jirginsa,' Shettima Ya Fasa Zuwa Taron da Tinubu Ya Turasa Wakilci

'Wani Abu Ya Samu Jirginsa,' Shettima Ya Fasa Zuwa Taron da Tinubu Ya Turasa Wakilci

  • An soke tafiyar mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima zuwa birnin Samoa domin wakiltar Najeriya a taron CHOGM na 2024
  • Fadar shugaban kasa ta sanar da cewa an soke tafiyar Shettima zuwa Samoa bayan wani 'bakon abu' ya afkawa jirginsa a Amurka
  • A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana matakin da Tinubu ya dauka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya soke tafiyarsa zuwa taron shugabannin kasashen Commonwealth na shekarar 2024 a kasar Samoa.

Shugaba Bola Tinubu ne ya wakilta mataimakin nasa domin ya wakilci kasar a taron kungiyar kasashe 56 da suka samu raino daga Ingila.

Kara karanta wannan

Tsohon gwamna Shekarau ya fadi dalilin sabuwar tafiyar siyasa a Arewa

Fadar shugaban kasa tga yi magana kan tafiyar Shettima zuwa taron CHOGM
Shettima ya fasa zuwa taron Commonwealth bayan wani bakon abu ya fada kan jirginsa. Hoto: @KashimSM
Asali: Twitter

Wani abu ya samu jirgin Shettima

Duk da wannan umarni na Tinubu, jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa fadar shugaban kasa ta sanar da cewa an soke tafiyar Shettima zuwa Samoa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An soke tafiyar Shettima zuwa Samoa bayan wani 'bakon abu' ya afkawa jirginsa a lokacin da ya tsaya a filin jirgin sama na JFK a birnin New York na kasar Amurka.

Kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya fitar a jiya, ya bayyana cewa, 'bakon abun' ya lalata gilashin jirgin saman.

Shettima ba zai je taron CHOGM ba

Sanarwar ta ce Shugaba Tinubu ya dauki matakin gaggawa, inda ya tura tawagar ministoci domin su wakilici Najeriya a taron na CHOGM da ke gudana a Samoa, birnin Apia.

Jaridar This Day ta kuma ruwaito cewa sanarwar ta ce an fara gyara jigrin mataimakin shugaban kasar da ya samu matsala.

Kara karanta wannan

Gyaran tattalin arziki: Manyan nasarori 5 da gwamnatin Tinubu ta samu a 2024

"Wani bakon abu ya lalata gilashin bangaren direbobin jirgin saman.
“Ministan muhalli, Balarabe Abass Lawal ne zai jagoranci tawagar Tinubu ya tura domin ta wakilci Najeriya a taron Commonwealth na 2024 (CHOGM) a Samoa."

- A cewar sanarwar Onanuga.

Tinubu ya tura Shettima taron CHOGM

Tun da fari, mun ruwaito cewa Shugaba Bola Tinubu ya umurci mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya wakilce shi a wajen taron CHOGM.

An tsara cewa Kashim Shettima zai haɗu da Sarki Charles na Ingila da sauran shugabannin duniya daga ƙasashe mambobi 56 a taron na kungiyar Commonwealth.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.