An yi Sauyi a Masallacin Manzon Allah SAW: An Nada Limamai a Makka da Madina

An yi Sauyi a Masallacin Manzon Allah SAW: An Nada Limamai a Makka da Madina

  • Gwamnatin kasar Saudiyya ta yi sauye sauye a masallatai masu alfarma na Makka da Madina a ranar Alhamis
  • Rahotanni sun nuna cewa an nada sababbin limaman dindindin da za su rika jagorantar salla a masallatai masu alfarma
  • Sheikh Muhammad Bahraj na cikin waɗanda aka naɗa domin limanci a masallacin Annabi SAW da ke birnin Madina

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Saudi Arabia - Hukumomi a kasar Saudiyya sun yi sauye sauye a masallatai masu alfarma na Makkah da Madina.

A yau Alhamis, 30 ga watan Rabiu Auwal 1446, gwamnatin Saudiyya ta fitar da sanarwa kan nada sababbin limamai a kasar.

Makka
An nada limamai a Makka da Madina. Hoto: Inside the Haramain
Asali: Facebook

Legit ta tattaro bayanai kan limaman da aka naɗa ne a cikin wani sako da shafin kasar Saudiyya na Inside the Haramain ya wallafa a Facebook.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya koka da karuwar talauci a Arewa duk da yan siyasarta na gwamnati

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An nada limamai a Makka da Madina

Gwamnatin kasar Saudiyya ta nada sababbin limamai guda hudu a masallatai masu alfarma na kasar.

Sababbin limaman za su cigaba da jan sallah da sauran ayyukan addinin Musulunci a manyan masallatan kasar.

Sunayen sababbin limaman da aka nada a Makka

Gwamnatin Saudiyya ta nada Sheikh Badar Al-Turki a matsayin sabon limamin masallacin Makka mai alfarma.

Haka zalika gwamnatin Saudiyya ta nada Sheikh Waleed Al-Shamsan a matsayin sabon limami a masallacin na harami.

Limanan masallacin Manzon Allah SAW a Madina

Kasar Saudiyya ta nada Sheikh Muhammad Bahraj a matsayin limamin dindindin a masallacin Manzon Allah SAW.

A daya bangaren, an nada Sheikh Abdullah Al-Quraafi a matsayin sabon limamin dindindin a masallacin da ke Madina.

An canza tsare tsaren aikin Hajji

A wani rahoton, kun ji cewa NAHCON ta sanar da wani tsari da hukumomin ƙasar Saudiyya suka kawo wanda za a fara aiwatarwa a 1446.

Kara karanta wannan

Gwamna zai fara biyan albashin N70,000 a Oktoba, dalibai za su yi karatu kyauta

Mai magana da yawun hukumar NAHCON, Fatima Usara ta ce daga yanzu ciyarwa da ɗakunan kwanan alhazai sun koma hannun Saudiyya.

An ruwaito cewa Usara ta ce tuni shirye-shiryen hajjin suka yi nisa kuma hukumar ta zauna da wakilan jihohi kan wannan sabon tsari.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng