"Kun Wahalar da Alhazai, Gwamna Ya Ɗauki Zafi Yayin da Ya Yi Barazana ga NAHCON
- Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed ya koka kan yadda alhazai suka tsinci kansu a Saudiyya a bana
- Gwamnan ya soki tsarin hukumar NAHCON inda ya ce ya kamata a ba jihohi ragamar kula da alhazansu domin samar musu da walwala
- Legit Hausa ta tattauna da wani mahajjaci daga jihar Gombe kan tsare-tsaren hukumar kula da alhazai ts NAHCON
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Makkah, Saudiyya - Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya caccaki hukumar alhazai ta kasa (NAHCON).
Bala ya nuna damuwa kan yadda hukumar ta ba mahajjatan kunya a Saudiyya ganin yadda ta ke tafiyar lamarin a bana.

Source: Facebook
Bauchi: Bala ya koka kan tsare-tsaren NAHCON

Kara karanta wannan
Gwamna ya dauki tsattsauran mataki kan masallatai da coci a Plateau, ya kakaba doka
Sanata Bala ya bayyana haka ne yayin zantawa da mahajjatan jihar Bauchi a Mina da ke Makkah a kasar, cewar Tribune.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Gwamnan ya bukaci gyara kan ayyukan hukumar domin samun sauyi a yadda take gudanar da ayyukanta, kamar yadda Punch ta tattaro.
Har ila yau, gwamnan ya bukaci a bar gwamnatocin jihohi su na kula da alhazansu tun da ta jiha suke biyan kudin aikin hajji.
Ya bayyana damuwa kan yadda mahajjata suka fuskanci wahalhalu saboda tsare-tsaren hukumar da sauran masu ruwa da tsaki.
Gwamna Bala ya yi barazana ga NAHCON
Tsohon Ministan ya ba da misalin yadda hukumar ta ba alhazai dala 500 a matsayin alawus na tafiye-tafiye duk da N8m da suka karba a hannun alhazan.
Daga bisani, gwamnan ya ce zai hada kai da sauran gwamnoni domin kwace ikon hukumar idan ba ta sauya tsarin da take tafiya a kai ba.
Sanata Bala ya yi amfani da wannan dama inda ya ba alhazan jiharsa 2,689 riyal 300 kowannensu a matsayin goron sallah.

Kara karanta wannan
Ba a gama da rigimar sarautar Kano ba, Gwamna ya yi dokar dakile tasirin sarakuna
Tattaunawar wakilin Legit Hausa da wani Alhaji
Legit Hausa ta tattauna da wani mahajjaci daga jihar Gombe kan tsare-tsaren hukumar NAHCON
Alhaji Muhammad Abdullahi ya ce shi ba yau ya fara zuwa ba amma a gaskiya an samu matsaloli da dama.
"Kullum kara inganta abubuwa ake yi a Saudiyya amma bana an dan samu matsaloli musamman daga ɓangaren hukumar NAHCON."
"Musamman yawan mace-mace da aka samu duk da ƙaddara ne daga Allah kuma ba iya Najeriya ba ne."
"Na ji wasu gwamnoni suna korafi tare da kiran a basu kula da alhazansu, idan har za a bi tsari hakan ba matsala ba ne."
- Muhmmad Abdullahi
Abba ya ba mahajjata riyal 100
A wani labarin, kun ji cewa Gwamna Abba Kabir ya ba mahajjatan jihar Kano 3,121 goron sallah a kasar Saudiyya.
Abba ya ba kowane mahajjaci riyal 100 domin gudanar da Sallah cikin walwala yayin da suke kasa mai tsarki domin aikin hajji.
Asali: Legit.ng