Girgizar Kasa Mai Karfin Gaske Ta Halaka Mutum 632 a Kasar Morocco
- An samu aukuwar iftila'in girgizar ƙasa mai ƙarfin gaske a yankin birnin Marrakesh na ƙasar Morocco
- Girgizar wacce ke da ƙarfin maki 6.8 ta auku ne a tsakar daren ranar Juma'a, 8 ga watan Satumban 2023
- Ma'aikatar harkokin cikin gidan ƙasar ta tabbatar da cewa adadin mutanen da suka rasu ya kai, 632 yayin da wasu mutum 380 suka samu raunika
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Marrakesh, Morocco - An samu girgizar ƙasa mai ƙarfin gaske a birnin Marrakesh na ƙasar Morocco, a tsakar daren ranar Juma'a, 8 ga watan Satumban 2023.
Mutanen da suka riga mu gidan gaskiya a sakamakon girgizar ƙasar ya ƙaru zuwa sama da mutum 632, rahoton Sky News ya tabbatar.

Asali: Facebook
A cewar bayanai daga ma'aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar, wasu mutum 329 sun samu raunika, inda mutum 51 ke cikin mawuyacin hali.

Kara karanta wannan
An Tafka Barna: Kakakin Majalisa Ya Bayyana Asarar Da Najeriya Ta Tafka a Dalilin Satar Man Fetur
Ma’aikatar ta tabbatar da cewa girgizar ƙasar wacce ke da ƙarfin maki 6.8, ta yi ɓarna a yankunan Marrakesh, Al-Haouz, Azilal, Ouarzazate, Taroudant da kuma Chichaoua.
DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka
Jama'a da dama sun tserewa gidajensu a cikin dare domin kuɓutar da rayukansu, yayin da ake cigaba da aikin ceto, cewar rahoton Aljazeera.
Girgizar ƙasar mai karfi wacce ta auku a Marrakesh, yankin da masu yawon buɗe ido ke yawan zuwa, ta kwashe kusan mintuna 10, sannan an ji motsi a wasu biranen ƙasar da suka haɗa da Rabat, Casablanca da kuma Essaouira.
Ba a taɓa girgizar ƙasa irinta ba a ƙasar
Wakilin jaridar Sky News yana cikin birnin Marrakesh lokacin da iftila'in girgizar ƙasar ya auku a daren na ranar Juma'a.
Ya bayyana cewa girgizar ƙasar ta zarce dukkanin waɗanda ya taɓa gani sun auku a Morocco, inda ba a cika samun iftila'in girgizar ƙasa ba.
"Tana da ƙarfi sosai, ban taɓa ganin wanu abu makamancinta ba, tana da matuƙar ƙarfi sosai." A cewarsa.
Ya kuma bayyana cewa wasu mutanen sun kwana a tituna saboda tsoron ka da gidajensu su ruguje.
An Samu Girgizar Kasa a Siriya Da Turkiyya
A wani labarin kuma, an sake samun wata sabuwar girgizar kasa da ta auku a iyakar kasashen Turkiyya da Siriya, kwanaki bayan afkuwar ta faro da mutane sama da 40,000 suka kwanta dama a kasashen biyu.
Girgizar kasar mai girman 6.4 ta daki yankin Hatau ne na kasar Turkiyya, wacce ta yi barna a makwanni biyu da suka gabata.
Asali: Legit.ng