Shugaba Zelensky Ya Taya Bola Tinubu Murnar Lashe Zabe, Ya Gayyace Shi Zuwa Ukraine

Shugaba Zelensky Ya Taya Bola Tinubu Murnar Lashe Zabe, Ya Gayyace Shi Zuwa Ukraine

  • Bola Ahmad Tinubu, zababben shugaban kasan Najeriya ya karbi sakon taya murna daga shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensyky
  • Zelensky ya kuma gayyaci Tinubu zuwa kasar Ukraine da ke Gabashin Turai saboda wasu dalilai
  • Idan baku manta ba, Tinubu ya ce zai yi gogayya da Rasha wajen samar da iskar gas ta Turai, akwai tsama tsakanin Ukraine da Rasha

Birnin Kif, kasar Ukraine - Shugaban kasar Ukriane, Volodymyr Zelensky ya aike da sakon taya murnar lashe zabe ga Bola Ahmad Tinubu na Najeriya bayan zaben ranar 25 ga watan Faburairu.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da kafar yanar gizon kamfen Tinubu/Shettima ta yada a ranar Alhamis 20 Afirilu, 2023.

A cewar sanarwar, Zelensky ya yaba da yadda aka yi zaben Najeriya cikin kwanciyar hankali da lumana, wanda ya kai ga nasarar Tinubu.

Kara karanta wannan

Zaben Adamawa: Zababben Shugaban kasa, Tinubu ya yi kira ga ‘Yan Sanda da Binani

Zelensky ya gayyaci Tinubu Ukraine
Shugaba Zelensky na Ukraine da sabon shugaban Najeriya Tinubu | Hoto: Bola Ahmad Tinubu
Asali: Twitter

Sakon Zelensky ta Tinubu game da zaben 2023

Shugaban na Ukraine, ya kuma bayyana shirin kasarsa na ci gaba da hulda da Najeriya a karkashin jagorancin Bola Tinubu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A sakonsa na fatan alheri, Zelensky ya mika sakon gayyata ga Tinubu zuwa kasar Ukraine bayan rantsar dashi a ranar 29 ga watan Mayu.

A cewar wani yankin sanarwar ya ce:

“Duba da wannan damar, ina gayyatar da ka kawo ziyarar aiki zuwa Ukraine a duk lokacin da ka samu dama.”

Yiwuwar Tinubu ya ziyarci Ukraine

Shugaban na Ukraine ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa cewa, gwamnati Tinubu za ta mutunta gayyatarsa don kara dankon zumunci tsakanin kasashen biyu.

Hakazalika, ya ce yana son gwamnatin Tinubu ya shiga a dama da ita a shirin Ukraine na kai hatsi kasashen Afrika don habaka samar da abinci.

Tsawon kwanaki 421 kenan yanzu, kasar Rasha ta kai farmakin mamaya kan al’ummar kasar Ukraine da basu ji basu gani ba, lamarin da ya sa Tinubu yace zai yi gasa da Rasha a fannin makamashi.

Kara karanta wannan

Karfin hali: Matashi dan Arewa ya daura damara, zai yi tattaki daga jiharsu don shaida rantsar da Tinubu

Rasha na son wagaza kasata, inji shugaba Zelensky

A wani labarin, kunji yadda shugaban kasar Ukriane ya bayyana shirin Rasha na ci gaba da farmakar kasarsa ba sassautawa.

Ya bayyana cewa, shugaba Putin na Rasha na ci gaba da shirin yadda zai karar da kasarsa ta Ukraine.

Ana ta yaki tsakanin kasashen biyu tun a watan Faburairun shekarar da ta gabata, hakan ya girgiza duniya ta bangarori daban-daban.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.