Sunaye, hotuna da bidiyoyin kira'ar limamai 6 na Masallacin Annabi da ke Madina
Ba tare da tantama ba, zama limamin masallacin Annabi shi ne abu mafi girma, karramawa da alfahari a duniyar Musulunci baki daya. Ba kowa Allah madaukakin Sarki ke bai wa irin wannan damar da karamar ba.
![Jerin sunaye da hotunan limami 6 na Masallacin Annabi da ke Madina Jerin sunaye da hotunan limami 6 na Masallacin Annabi da ke Madina](https://cdn.legit.ng/images/1120/3ab8af2a62adfe41.jpeg?v=1)
Asali: UGC
Sharuddan zama limamin masallacin Annabi
Duk da gwamnatin Saudi Arabiya ce ke nada limamai, dole ne a cike wadannan ka'idojin hudu kafin zama limamin masallacin Annabi, kamar yadda Argaam suka ruwaito.
- Kasancewar mutum mazaunin kasar Saudi na dindindin.
- Kaiwa shekaru 30 ko sama da haka.
- Mallakar digiri a fannin shari'a daga wata jami'ar Saudi.
- Haddace Qur'ani da kira'a mai dadi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
1. Sheikh Abdul Mohsen Al Qasim
An haifi Sheikh Abdul Mohsen bin Muhammad bin Abdul Rahman bin Muhammad bin Abdullah bin Qasim a 1968 sannan ya haddace kur'ani da karancin shekaru.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/bc9f31f8986015fd.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Tsohon zakaran kwallon Afrika, Patrick Mboma, ya musulunta kuma kai tsaye aka aura masa amarya
Ya mallaki kwalin digiri a fannin shari'ar musulunci, sannan an nada shi a matsayin limamin masallacin Annabi a shekarar 1997.
2. Sheikh Saleh Al Badir
An haifi Sheikh Saleh Al Badir a shekarar 1970 a Hofuf. Ya yi digirinsa na farko a fannin shari'a daga jami'ar musulunci ta Muhammad Bin Saud.
An nada shi a matsayin limamin, kuma mai wa'azi a masallacin Annabi a shekarar 1998. Ya dauki tsawon lokaci yana jagorantar sallolin Tarawihi a masallacin Annabi tun shekarar 2005.
3. Sheikh Ahmed Bin Humaid
An haifi Sheikh Ahmed Bin Talib bin Abdul Hamid bin Al Muzaffar Khan a shekarar 1980 a Riyadh. Ya yi digirin digirgirgir a fannin da ya shafi shari'a daga babbar cibiyar shari'a.
An nada shi a cikin watan Ramadanan shekarar 1434 don ya jagoranci sallolin Tarawihi da Tahajjud a masallacin Annabi, daga bisani aka nada shi limami a ranar 9 ga watan Oktoba, 2013.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/08a79dbd54b52d78.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Yanzu-Yanzu: Shugaban ƙasa Buhari ya naɗa sabon shugaban masu yi wa kasa hidima NYSC
4. Sheikh Abdullah bin Abdul Rahman
A halin yanzu, Abdullah bin Abdul Rahman bin Suleiman Al-Baijan na limancin masallacin Annabi, sannan yana daya daga cikin mambobin reshen jami'ar musulunci ta Madina.
An nada shi a matsayin limamin masallacin Annabi a shekarar 2013, sannan ya yi digirin digirgirgir a sashin shari'ar siyasa daga jami'ar musulunci ta Imam Muhammad bin Saud a shekarar 2015.
5. Sheikh Khaled Al Muhanna
An haifi Khalid bin Suleiman bin Abdullah bin Suleiman bin Muhanna Al-Shamkari a Al Ahsa a shekarar 1976. Ya yi digirin digirgirgir daga jami'ar musulunci ta Imam Muhammad bin Saud a shekarar 2010.
An nada Sheikh Khalid Al Muhanna a matsayin limamin masallacin Annabi a ranar 13 ga watan Oktoba 2019.
6. Sheikh Ahmed bin Ali Al-Hudhaifi
Sheikh Dr. Ahmed bin Ali Al-Hudhaifi limami ne, kuma mai bada shawara, sannan wakilin dake kula da jagoranci da al'amuran babban masallacin Annabi.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/6a1738d1aadde030.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Yadda Jam’iyyar APC ta samu tayi wa Yari, Marafa da Gwamna Matawalle sulhu a Zamfara
Ramadan 2022: Sunayen limaman da za su jagoranci Tarawih da Tahajjud a Masjid Al Haram
A wani labari na daban, hukumomin kasar Saudiyya sun saki sunayen limaman da za su jagoranci sallolin Tarawihi da Tahajjud a masallacin Harami dake Makkah na watan Ramadanan wannan shekarar. Sakin jerin sunayen limaman yazo ne ta shafin a ranar 23 ga watan Maris.
Jerin sunayen limaman da zasu jagoranci sallar Tarawihi da Tahajjud a masallacin Harami sun hada da.
Asali: Legit.ng