PDP ta caccaki gwamna, mataimakiyarsa da kakakin majalisa bisa barin jama'arsu don tare wa a kasar waje

PDP ta caccaki gwamna, mataimakiyarsa da kakakin majalisa bisa barin jama'arsu don tare wa a kasar waje

  • A halin yanzu, da alama babu kowa a kasa wanda zai yi aiki a matsayin shugaban gwamnatin jihar Ogun
  • Wannan ya kasance ne saboda gwamnan jihar, mataimakiyarsa, da kakakin majalisar ba sa Najeriya
  • Gwamna Dapo Abiodun da Noimot Salako-Oyedele suna Burtaniya yayin da kakakin majalisar, Olakunle Oluomo, ke Amurka

Da take Allah wadai da wannan, PDP reshen Ogun ta ce wannan shine babban rashin sanin yakamata a harkokin mulki

Rashin kasancewar Gwamna Dapo Abiodun, mataimakinsa, Noimot Salako-Oyedele, da kakakin majalisar dokokin Ogun, Olakunle Oluomo, a jihar na haifar da damuwa sosai a jihar.

PDP ta caccaki gwamna, mataimakiyarsa da kakakin majalisa bisa barin jama'arsu don tare wa a kasar waje
PDP ta caccaki gwamna, mataimakiyarsa da kakakin majalisa bisa barin jama'arsu don tare wa a kasar waje Hoto: Ogun State House of Assembly
Asali: UGC

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Abiodun ya bar kasar zuwa Burtaniya don kai ziyarar ban girma ga Asiwaju Bola Ahmed Tinubu kwanan nan yayin da Salako-Oyedele ke London.

Bugu da kari, an ce Oluomo yana Amurka don taron kasa da kasa.

Kara karanta wannan

Tsohon Saurayi ya aikewa Ango tsaffin hotunan amaryarsa kan ta tuba, aure ya mutu

Wannan gibi da aka samu a manyan kujeru uku na jihar ya haifar da tsoro, tashin hankali, da zafin martani daga mutane da yawa.

Jaridar ta kuma rahoto cewa a nata bangaren, jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta bayyana lamarin a matsayin "karshen rashin sanin ya kamata a harkokin mulki."

Wannan shi ne jawabin shugaban jam’iyyar PDP na Ogun, Sikirulahi Ogundele, wanda ya zanta da manema labarai kan lamarin mai tayar da hankali.

Ogundele ya ce:

“Gwamna ya yi tafiya, mataimakinsa da kakakin majalisa sun bi shi; gaskiya, ban yi takaici ba tunda ba su da alkibla tunda ba su da hangen nesa. Ban ji takaici ba.
"Za a fara bikin ranar 'yancin kai na shekara-shekara a ranar Juma'a, kawai su koma jihar Ogun su yi bikin ranar."

Kara karanta wannan

Yadda jami'an tsaron UNIMAID suka afka dakunan kwanan dalibai mata, suka damke masu zanga-zanga

A wani labari na daban, gabanin bikin cika shekaru 61 da samun ‘yancin kai, gwamnatin tarayya ta sanar da cewa za a rufe wasu sassan sakatariyarta da ke Abuja.

Jaridar The Punch ta ruwaito cewa anyi hakan ne a wani bangare na kokarin tabbatar da bikin samun 'yancin kai a ranar Juma'a, 1 ga watan Oktoba cikin nasara.

Legit.ng ta tattaro cewa ginin sakatariyar yana kusa da dandalin Eagles Square kuma cewa za a gudanar da babban taro na 'yancin kai a ranar Juma'a a wajen.

Asali: Legit.ng

Online view pixel