Da Dumi-Dumi: Shugaban Majalisar Dattijai Ya Rantsar da Sabon Sanatan Jam'iyyar PDP

Da Dumi-Dumi: Shugaban Majalisar Dattijai Ya Rantsar da Sabon Sanatan Jam'iyyar PDP

  • Shugaban majalisar dattijan Najeriya, Sanata Ahmad Lawan, ya bada rantsuwar kama aiki ga sabon sanata daga Cross Rivers
  • Sanatan wanda kotun koli ta tabbatar da sahihancin takararsa karkashin PDP, ya fara aiki ne ranar Laraba
  • Sanata Agom Jarigbe zai maye gurbin wanda aka rantsar da farko, Steven Odey, daga mazaɓar Cross Rivers ta arewa

Abuja - Shugaban majalisar dattijai, Sanata Ahmad Lawan, ranar Laraba, ya rantsar da sabon sanatan jam'iyyar PDP, Agom Jarigbe, wanda zai maye gurbin, Stephen Odey, kamar yadda vanguard ta ruwaito.

Jarigbe na jam'iyyar hamayya ta PDP, ya jima suna fafatawa a shari'a da Steven Odey, kan waye halastaccen ɗan takarar da jam'iyya ta tsayar a zaɓen cike gurbin sanatan Cross Rivers ta arewa.

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Hotuna sun bayyana yayin da Buhari ya rantsar da sabbin kwamishinonin INEC

Jarigbe ya amshi rantsuwar fara aiki daga shugaban majalisar bayan samun nasara a kotun ƙoli ta ƙasa, kamar yadda dailytrust ta ruwaito.

Lawan Ya Rantsar da Sabon Sanatan PDP
Da Dumi-Dumi: Shugaban Majalisar Dattijai Ya Rantsar da Sabom Sanatan Jam'iyyar PDP Hoto: thecable.ng
Asali: UGC

Meyasa INEC ta gudanar da zaɓen cike gurbi?

Legit.ng Hausa ta gano cewa hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta gudanar da zaɓen maye gurbi ne a mazaɓar Cross Rivers ta arewa bayan mutuwar sanata Rose Oko.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Sai dai kotun ɗaukaka ƙara dake zamanta a Kalaba, babban birnin jihar, ta bayyana, Jarigbe Agom Jarigbe a matsayin ɗan takarar da ya lashe zaben cike gurbi na ranar 5 ga watan Disamba, 2020.

Kotun bisa jagorancin mai shari'a Chioma I. Nwosu, ta bada umarnin a ba shi satifiket ɗin zaɓe, wanda da farko hukumar INEC ta baiwa, Steven Odey.

Bugu da kari kotu ta umarci INEC ta kwace satifiket ɗin daga hannun wanda ta baiwa da farko, ta baiwa wanda hukuncin kotu ya tabbatar a matsayin zaɓaɓɓen sanata.

Kara karanta wannan

Dan Majalisar Tarayya Ya Rigamu Gidan Gaskiya, Majalisa Ta Tafi Hutu Saboda Jimami

A wani labarin na daban kuma Ministan Buhari ya fallasa yadda ake amfani da jiragen alfarma wajen satar albarkatun Zinari a Najeriya

Ministan hakar albarkatun ƙasa, Dakta Uche Ogah, ya bayyana irin ta'adin da ake yi ta hanyar amfani da jirage masu zaman kansu.

Ogah yace dole sai an samar da hukunci mai tsauri kan duk waɗanda aka damke da hannu a safarar zinari ba bisa ka'ida ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel