Zaben 2023: Jigon APC ya yi kakkausar gargadi ga shugabannin jam’iyyar mai mulki

Zaben 2023: Jigon APC ya yi kakkausar gargadi ga shugabannin jam’iyyar mai mulki

  • Jigon jam'iyyar APC, Cif Ben Adaji ya gargadi shugabannin jam'iyyar a kan tursasa 'yan takara a zaben 2023
  • Adaji ya ce yin hakan zai kawo hargitsi tare da tarwatsa jam'iyyar
  • Ya kuma yi misali da abun da ya samu babbar siyasar adawar kasar a 2019 wanda ya kai ta ga shan kaye

Taraba - Cif Ben Adaji, jigo a jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a Taraba, ya gargadi jam'iyyar game da tursasa 'yan takara da shugabannin jam'iyyar gabanin zaben 2023.

Adaji ya fadi haka ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a Jalingo ranar Alhamis, 9 ga watan Satumba, PM News ta ruwaito.

Zaben 2023: Jigon APC ya yi kakkausar gargadi ga shugabannin jam’iyyar mai mulki
Zaben 2023: Jigon APC ya yi kakkausar gargadi ga shugabannin jam’iyyar mai mulki Hoto: APC
Source: Facebook

Babban jigon jam’iyyar mai mulki, wanda ya kasance tsohon dan takarar kujerar dan majalisar wakilai ne na mazabar Ankpa, Omala da Olomaboro a Kogi, ya ce abubuwan da suka faru a baya sun nuna cewa yin hakan yana haifar da mummunan sakamako.

Kara karanta wannan

Babbar magana: 'Yan APC sama da 50,000 sun sauya sheka zuwa PDP a Adamawa

Rahoton ya ce Adaji ya lura cewa faduwar jam'iyyar adawa ta Peoples Democratic Party (PDP) a shekarar 2019, galibi ya faru ne sakamakon tursasa 'yan takara da shugabannin jam'iyyar.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya shawarci shugabancin jam’iyyar APC da ta baiwa mambobi damar zabar shuwagabannin su a dukkan matakai tare da kaucewa tursasa ‘yan takarar da basu da farin jini a lokacin zabe.

Adaji ya kuma bukaci APC da ta yi taka tsantsan da wasu mambobin da suka fice daga wasu jam’iyyun siyasa, domin suna iya haifar da matsaloli a jam’iyyar.

Ya ce:

"Muna son APC ta bambanta da PDP a duk gudanarwarta don kayar da PDP.
“Tunda APC ta kwace mulki daga hannun PDP, babbar jam’iyyar siyasa a Afirka, hakan na nufin mutane suna kallon jam’iyyar a matsayin mafi kyawun madadin PDP.
“Don haka, dole APC ta yi taka -tsantsan wajen gudanar da dukkan ayyukanta ba tare da nuna son kai da rashin adalci ba.
“Ina ba da shawara ga jami’an jam’iyyar a dukkan matakai da su ba da damar gwabzawa ga masu son yin takara don gwada karfinsu da farin jinin su.”

Kara karanta wannan

2023: Wasu manyan jiga-jigan PDP 3 sun sake sauya sheka zuwa APC

Tsohon ‘dan takarar Shugaban kasa ya samu matsayi daga sauya-sheka zuwa APC

A wani labarin, tsohon ‘dan takarar shugaban kasa, Gbenga Olawepo-Hashim yana cikin wadanda aka zaba a matsayin wakilan jam’iyyar APC.

Gbenga Olawepo-Hashim ya zama daya daga cikin wakilan jam’iyyar APC na kasa a zaben shugabannin kananan hukumomi da aka yi kwanan nan.

Rahoton yace Olawepo-Hashim zai wakilci mazabar Bwari a babban birnin tarayya Abuja tare da shugaban gunduma, Ali Shere da kuma wasu mutum biyu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng