Tsohon ‘dan takarar Shugaban kasa ya samu matsayi daga sauya-sheka zuwa APC

Tsohon ‘dan takarar Shugaban kasa ya samu matsayi daga sauya-sheka zuwa APC

  • Gbenga Olawepo-Hashim ya shiga cikin wakilan APC a birnin tarayya APC
  • An zabi Olawepo-Hashim ne a zaben kananan hukumomin da APC ta shirya
  • Sauran shugabannin jam’iyyar na mazabar Bwari sun koma kan kujerunsu

Abuja- The Nation ta ce tsohon ‘dan takarar shugaban kasa, Gbenga Olawepo-Hashim yana cikin wadanda aka zaba a matsayin wakilan jam’iyyar APC.

Gbenga Olawepo-Hashim ya zama daya daga cikin wakilan jam’iyyar APC na kasa a zaben shugabannin kananan hukumomi da aka yi kwanan nan.

Rahoton yace Olawepo-Hashim zai wakilci mazabar Bwari a babban birnin tarayya Abuja tare da shugaban gunduma, Ali Shere da kuma wasu mutum biyu.

An gudanar da wannan zabe ne a WSH Hotel da ke unguwar Bwari a karshen makon da ya wuce.

Kara karanta wannan

Yadda jam’iyyar APC ta tsunduma a rikita-rikita a Jihohi 16 bayan zaben Shugabanni

Gbenga Olawepo-Hashim ya samu mukami a APC

Kamar yadda Daily Trust ta wallafa, dukkanin sauran masu rike da mukamai a jam’iyyar APC a mazabar sun dawo kan mukamansu ba tare da hamayya ba.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Da yake magana bayan an zabe shi a matsayin wakili, Gbenga Olawepo-Hashim ya gode wa ‘ya ‘yan jam’iyyar APC, ya kuma yi kira a ajiye kayan fada.

Taron APC
Cinkoso a wajen taron APC a Taraba Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

‘Dan siyasar ya roki duk masu korafi game da yadda aka gudanar da zaben fitar da gwanin ‘dan takarar shugabannin kananan hukumomi su yi hakuri.

An rahoto Olawepo-Hashim yana yabon wadanda suka zo zaben, kuma ya roki daukacin ‘ya ‘yan jam’iyyar APC su hada kai a zaben kananan hukumomi.

Wadanda suka halarci wannan zabe sun hada da Hon. Shekwolo Ushafa, Bwari, Idris Umar Farouk, Hon. Adami Ayenajeyi da kuma Hon. Musa Dikko.

Kara karanta wannan

Jigon APC ya bayyana wanda ya dace da mulki, ya cire Osinbajo, Tinubu a lissafin 2023

Jawabin da Gbenga Olawepo-Hashim ya yi

“Ina rokon fusatattun ‘ya ‘yan jam’iyyar mu mai daraja ta APC, su ajiye kayan fada, su hada-kai, su yi aiki da shugabannin da aka zaba.”
“Jimillar karfin tattalin arzikin Najeriya yana bunkasa, ina mai tabbatar maku da cewa APC na aikin kokari domin farfado da tattalin kasa.”

Amaechi/Zulum a 2023?

Kwanan nan aka ji jigon APC, Sanata Alex Kadiri yana fada wa ‘Yan siyasan Arewa, Ibo da na Yarbawa su hakura da neman kujerar shugaban kasa a 2023.

A cewarsa, babu wani ‘Dan siyasan Arewa ta tsakiya da zai iya rike shugaban kasa. Kadiri yana ganin Rotimi Amaechi da Umara Zulum za su iya kai labari.

Asali: Legit.ng

Online view pixel