Tsohon ‘dan takarar Shugaban kasa ya samu matsayi daga sauya-sheka zuwa APC

Tsohon ‘dan takarar Shugaban kasa ya samu matsayi daga sauya-sheka zuwa APC

  • Gbenga Olawepo-Hashim ya shiga cikin wakilan APC a birnin tarayya APC
  • An zabi Olawepo-Hashim ne a zaben kananan hukumomin da APC ta shirya
  • Sauran shugabannin jam’iyyar na mazabar Bwari sun koma kan kujerunsu

Abuja- The Nation ta ce tsohon ‘dan takarar shugaban kasa, Gbenga Olawepo-Hashim yana cikin wadanda aka zaba a matsayin wakilan jam’iyyar APC.

Gbenga Olawepo-Hashim ya zama daya daga cikin wakilan jam’iyyar APC na kasa a zaben shugabannin kananan hukumomi da aka yi kwanan nan.

Rahoton yace Olawepo-Hashim zai wakilci mazabar Bwari a babban birnin tarayya Abuja tare da shugaban gunduma, Ali Shere da kuma wasu mutum biyu.

An gudanar da wannan zabe ne a WSH Hotel da ke unguwar Bwari a karshen makon da ya wuce.

Kara karanta wannan

Yadda jam’iyyar APC ta tsunduma a rikita-rikita a Jihohi 16 bayan zaben Shugabanni

Gbenga Olawepo-Hashim ya samu mukami a APC

Kamar yadda Daily Trust ta wallafa, dukkanin sauran masu rike da mukamai a jam’iyyar APC a mazabar sun dawo kan mukamansu ba tare da hamayya ba.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Da yake magana bayan an zabe shi a matsayin wakili, Gbenga Olawepo-Hashim ya gode wa ‘ya ‘yan jam’iyyar APC, ya kuma yi kira a ajiye kayan fada.

Taron APC
Cinkoso a wajen taron APC a Taraba Hoto: guardian.ng
Source: UGC

‘Dan siyasar ya roki duk masu korafi game da yadda aka gudanar da zaben fitar da gwanin ‘dan takarar shugabannin kananan hukumomi su yi hakuri.

An rahoto Olawepo-Hashim yana yabon wadanda suka zo zaben, kuma ya roki daukacin ‘ya ‘yan jam’iyyar APC su hada kai a zaben kananan hukumomi.

Wadanda suka halarci wannan zabe sun hada da Hon. Shekwolo Ushafa, Bwari, Idris Umar Farouk, Hon. Adami Ayenajeyi da kuma Hon. Musa Dikko.

Jawabin da Gbenga Olawepo-Hashim ya yi

“Ina rokon fusatattun ‘ya ‘yan jam’iyyar mu mai daraja ta APC, su ajiye kayan fada, su hada-kai, su yi aiki da shugabannin da aka zaba.”

Kara karanta wannan

Jigon APC ya bayyana wanda ya dace da mulki, ya cire Osinbajo, Tinubu a lissafin 2023

“Jimillar karfin tattalin arzikin Najeriya yana bunkasa, ina mai tabbatar maku da cewa APC na aikin kokari domin farfado da tattalin kasa.”

Amaechi/Zulum a 2023?

Kwanan nan aka ji jigon APC, Sanata Alex Kadiri yana fada wa ‘Yan siyasan Arewa, Ibo da na Yarbawa su hakura da neman kujerar shugaban kasa a 2023.

A cewarsa, babu wani ‘Dan siyasan Arewa ta tsakiya da zai iya rike shugaban kasa. Kadiri yana ganin Rotimi Amaechi da Umara Zulum za su iya kai labari.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng